No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙara jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.

Tinubu ya faɗi haka ne a cikin jawabin da ya yi wa al’ummar ƙasar na ranar murnar cikar ƙasar shekara 63 da samun ‘yancin kai.

Ya ce za su kare rayukan ‘yan ƙasar ne ta hanyar tabbatar da jami’an tsaro sun yi aiki tare da kuma tattara bayanan sirri.

Shugaban na Najeriya ya kuma ce an ɗora wa hafsoshin tsaro nauyin ƙarfafa wa jami’ansu gwiwa wajen aiki tare.

“Ina jinjina tare da yaba wa jami’an tsaronmu kan yadda suke ba mu tsaro. Da yawa sun sadaukar da rayukansu don kare ƙasarmu. Muna tunawa da su a yau da kuma iyalansu.

Tinubu ya ce za a wadata sojoji da kayan aikin da ake buƙata domin su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...