Connect with us

Labarai

Za a kammala aikin titin jirgin ƙasa na Abuja a watan Mayun 2024 – Sakataren Sufuri

Published

on

Sakatariyar sufuri na hukumar babban birnin tarayya, (FCTA), ta bai lwa mazauna Abuja tabbacin samun isasshen tsaro a lokacin da titin jirgin ƙasa na Abuja ya fara aiki.

Sakataren sakatariyar, Ubokutom Nyah, ya ba da wannan tabbacin a ranar Laraba, bayan ya duba aikin gyaran layin dogo da ake yi a Abuja.

Kamfanin China Civil Engineering Construction Corporation Ltd., CCECC da ke gudanar da aikin gyaran ya kai ziyara ga mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya yi alƙawarin kammala aikin sufurin jiragen ƙasa na Abuja, ARMT, nan da watan Mayun 2024.

Mista Nyah ya ce samar da tsaro ya yi daidai da hangen nesa na sakatariyar tsaro.

Ya ƙara da cewa, tsaron rabon aikin layin dogo ya fi muhimmanci, inda ya ƙara da cewa an tsara dabarun tabbatar da hanyoyin jirgin.

KU KUMA KARANTA: Yadda Satar notunan titin Jirgin ƙasa ya kawo tangarɗa a sufuri (Bidiyo)

Ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa ayyukan kasuwanci da ake sa ran na titin jirgin ƙasa na Abuja zai fara aiki da wuri fiye da yadda ake tsammani.

Sakataren ya ce an gyara sassan hanyoyin da aka lalata, yayin da ake shigo da igiyoyin sadarwa.

“Muna fatan cewa wa’adin watanni tara da aka tsara zai zo a baya. Mazauna babban birnin tarayya Abuja na cikin wani babban abin mamaki da jin daɗi.

“Mun ratsa sama da kashi 60 cikin 100 na hanyoyin jiragen ƙasa kuma zan iya tabbatar da cewa an kammala sassan da aka lalatar da su yadda ya kamata.

“Ana gudanar da aikin share fage kuma an gaya min cewa igiyoyin sadarwa sun riga sun shiga tashar kuma nan ba da jimawa ba za su shigo.

“Kammala ARMT na iya zuwa da wuri fiye da yadda ake tsammani, saboda abin da muka gani a yau babban aiki ne,” in ji shi.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, sakataren tare da tawagarsa sun ziyarci tashoshin jiragen sama na Metro, Kukwuaba, filin jirgin sama da na Basango da dai sauransu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like