No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za a iya samun ambaliyar ruwa a jihohi 19 a faɗin Najeriya – Gwamnatin tarayya

Daga Jameel Lawan Yakasai

Gwamnatin tarayya ta yi hasashen cewa za a samu ruwan sama mai yawa na tsawon kwanaki biyar, wanda kan iya haddasa ambaliya a jihohi 19 da wurare 76.

Sashin kula da ambaliya na Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, ce ya fitar da wannan gargaɗi a jiya Talata, inda ya bukaci al’umma da masu ruwa da tsaki da su ɗauki matakan kariya cikin gaggawa.

KU KUMA KARANTA: Ambaliyar ruwa ta rushe gidaje da dama a garin Zakirai da ke Kano

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ambaliya mai muni ta afkawa jihohin Ogun da Gombe a ranar Talata, yayin da wasu jihohi kamar Legas, Filato, Anambra, da Delta su ma abin ya shafe su.

A cewar hasashen ambaliya da cibiyar ta bayar, za a iya samun ruwan sama mai ƙarfi wanda zai haifar da ambaliya daga 5 ga watan Agusta zuwa 9 ga Agusta, 2025, a waɗannan yankuna.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...