No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin jihar Kaduna ta jaddada shirinta na gudanar da aikin tiyatar cire marena ga mazajen da suka yi fyaɗe da kuma tiyatar salpingectomy ga takwarorinsu mata.

Ku tuna cewa a shekarar 2022, tsohon Gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya sanya hannu kan dokar da aka yi wa gyaran fuska ta 2020 wacce ta tanadi yin tiyatar cire marena ga maza da cire bututun fallopian ga mata masu yiwa yara fyaɗe bayan an same su da laifi.

A watan Nuwamba 2020, majalisar dokokin Kaduna ta amince da yanke hukunci a matsayin hukunci ga duk wanda aka samu da laifin fyade a jihar.

Kwamishiniyar aiyuka da ci gaban jama’a, Madam Rabi Salisu, ta bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki na jinsi da aka gudanar a Kaduna a ranar Alhamis 30 ga watan Nuwamba, 2023.

KU KUMA KARANTA: Kotu a Kebbi ta ɗaure yaron da ya yi wa ƙananan yara biyu fyaɗe

Ma’aikatarta ce ta shirya taron ƙolin, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Haɗin Kai da Shirye-shiryen Lafiya (CIHP).

Salisu ta ce matakin na ladabtarwa na ƙunshe ne a cikin dokar hana cin zarafin jama’a da gwamnatin jihar Kaduna ta kafa (VAPPL), ta shekarar 2018.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...