Za a binne gawarwaki 60 da ba a gano ’yan uwansu ba a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba.

Sashin Lafiya na ƙaramar hukumar Kaduna ta Kudu zai ɗauki gawarwakin don binnewa a a makabartar layin Bashama da ke unguwar Tudun Wada.

Mataimakiyar Sashin lafiya na ƙaramar hukumar Kaduna ta kudu – Asmau Saidu Adamu ta sanar cewa za a binne gawarwakin ne a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba da muke ciki.

“Za a ɗauko gawarwakin ne daga Asibitin Gwamna Awan zuwa Makabartar Bashama Road, ƙarƙashin jagorancin Kwamishinar Lafiya ta jihar Kaduna, Umma K Ahmed da Shugaban Asibitin Gwamna Awan, Dokta Gebriel Brown,” inji ta.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *