Connect with us

Labarai

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano zai sake duba batun tsige Sanusi – Kwankwaso

Published

on

Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce gwamnati mai zuwa a Kano za ta sake duba batun tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na 14.

Sanusi wanda ya zama sarki a wa’adin ƙarshe na Kwankwaso a matsayin gwamna, Gwamna mai barin gado Abdullahi Ganduje ne ya tsige shi, wanda shi ne mataimakin gwamna a lokacin da aka naɗa sarkin.

An cire Sanusi ne a ranar 9 ga Maris, 2020, sannan kuma an kore shi daga Kano aka aika shi zuwa garin Loko, wani yanki mai nisa a jihar Nasarawa, yayin da ake binciken kuɗaɗen masarautar da ke ƙarƙashinsa.

Ganduje ya kuma raba masarautun gida biyar ya naɗa sarakunan da suka yi daidai. Sai dai da yake magana a wani faifai na bidiyo, Kwankwao ya ce gwamnatin Abba Kabir Yusuf, zaɓaɓɓen gwamna, wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida, zai duba batun tsige masarautun.

KU KUMA KARANTA: 2023: Atiku, Kwankwaso, Obi da Tinubu sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya

“Mun yi yaƙin neman zaɓe kuma kamar yadda kuka sani muna da farin jini a Najeriya musamman a jihar Kano, yanzu mun dawo kuma in Allah Ya yarda za mu ci gaba da ayyukan alheri da gwamnatinmu ta bari.

Wannan gwamna mai jiran gado da tawagarsa za su ɗauke su.” “A matsayinmu na dattawa, za mu ci gaba da ba su shawarar yin abin da ya dace. Mun yi ƙoƙarin ka da a sa baki a batun kawo ko tsige wani sarki, amma yanzu dama ta zo.

“Waɗanda aka bai wa wannan dama za su zauna su duba batutuwan. Za su duba abin da ake sa ran yi. Bayan Sarki, hatta Masarautar ta rabu gida biyar. Duk waɗannan suna buƙatar yin nazari.

Galibi shugaba yakan gaji alheri, mummuna da al’amuran da suke da wuyar sulhu”. Ya kuma yi addu’ar Allah ya dafa wa Gwamna mai jiran gado damar tafiyar da al’amura cikin sauƙi.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Gwamnatin Kano ta mayar da martani ga NNPP | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamnatin Kano ta mayar da martani ga NNPP - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: Ganduje ba zai iya kallon idona kai tsaye ba, ni ubansa ne a siyasa – Kwankwaso | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like