Connect with us

Labarai

Yobe ta ɗage dokar haramcin hawa babur a wasu ƙananan hukumomin jihar

Published

on

Gwamnatin Jihar Yobe ta ɗage dokar hana hawa babura a Yobe ta Gabas, yankin da ya ƙunshi ƙananan hukumomi bakwai a jihar.

Ɗagewar ta soma aiki ne daga ranar Litinin, 6 ga Maris.

Sanarwar manema labarai wanda ofishin mataimaki na musamman ga Gwamna kan harkokin tsaro ya fitar, Brigadier General Dahiru Abdulsalam (Mai ritaya) ta nuna cewa, Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni shi ne ya amince da ɗage haramcin.

Ta ƙara da cewa, “An ɗage wannan haramci na hawa babur mai, daga yau 6 ga watan Maris 2023 a cikin ƙananan hukumomi bakwai da ke Yobe ta Gabas (Zone A) da suka haɗa da: Bursari, Damaturu, Geidam, Gujba, Gulani, Tarmuwa da Yunusari.”

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin jihar Yobe ta fara aikin tituna da magudanan ruwa

Haka kuma, sanarwar ta ce an dage haramcin bisa ga sharuɗɗan, “Baburan za su rinƙa aiki ne daga 6:00 na safe zuwa 6:00 na yamma a kowace rana.

“Sannan ba a lamunta a yi haya ko acaɓa da su ba. Kana kuma mutum ɗaya aka yarda ya hau ba tare da goyo ba.”

“Har wala yau kuma, dole duk masu babur su yi rijista tare da yankar lasisi da sauran ƙa’idojin mallaka a ƙaramar hukumar da mai babur ɗin yake ga hukumar kula da ababen hawa ta jihar Yobe (YOROTA) da hukumar bayar da lasisi ta jihar baki ɗaya. Sannan dole kowane mai babur ya tsaya iya ƙaramar hukumar da yake.”

Bugu da ƙari, sanarwar ta bayyana cewa, “Idan aka kama mai tuƙa babur ya ɗauki fasinja, za a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

“Sannan ba a yarda a yi zirga-zirga da babura daga wannan ƙaramar hukuma zuwa wacan ba, yin hakan saɓa doka ne.”

A ƙarshe, Dahiru Abdussalam ya bayyana cewa, “dukkan jami’an tsaro za su sanya ido domin tabbatar da jama’a sun bi doka sau da ƙafa.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: VIO sun kama babura sama da 300 da adaidaita 251 a Abuja | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like