Connect with us

Ƙasashen Waje

Yara biliyan 1.4 ne suke rayuwa cikin matsanancin talauci a duniya — MƊD

Published

on

Yara biliyan ɗaya da miliyan ɗari huɗu ƴan ƙasa da shekaru 16 ne a faɗin duniya suka gaza samun kowanne irin tallafin kariya na zamantakewar al’umma.

Wannan yanayin ya bar yaran cikin mawuyacin hali ta hanyar fuskantar cututtuka da rashin abinci mai gina jiki da kuma talauci, a cewar wani sabon rahoto da hukumomi biyu na Majalisar Ɗinkin Duniya tare da ƙungiyar agaji ta British Charity Save the Chirldren ta fita a ranar Laraba.

Ƙungiyar Ƙwadago ta Duniya (ILO) da Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) da Save the Children ne suka tattaro bayanan.

A ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi, ƙasa da kashi 10 cikin 100 na yara ne suke samun tallafin da ya kamata yara su samu, yanayin da ke nuna gagarumin bambanci da ke tsakani idan aka kwatanta da damarmakin da yara waɗanda ke ƙasashe masu arziki suke samu.

”A duniya baki ɗaya, akwai yara miliyan 333 da ke rayuwa cikin matsanancin talauci inda suke rayuwa kan kasa da dala 2.15 a kowace rana, sannan kusan yara biliyan daya ne suke fuskantar nau’in talauci iri daban-daban,” a cewar Natalia Winder Rossi, Darakta a sashen da ke kula da tsare-tsare da kuma samar wa al’umma kariya na UNICEF.

KU KUMA KARANTA: Australia ta goyi bayan ƙudurin MƊD na tsagaita wuta a Gaza

“A halin da ake ciki a yanzu, ba a kai ga cimma muradun ci gaba mai ɗorewa kan talauci ba, kuma ba za a amince da hakan ba,” in ji ta.

Rosi ta ce, kawo ƙarshen matsalar talauci tsakanin yara zaɓin tsari ne da gwamnatoci suke ɗauka.

Faɗaɗa ayyukan samar da kariya ga yara a yaƙin da ake yi da talauci yana da matuƙar muhimmaci, gami da samar da ci gaban kowanne yaro a duniya, in ji ta.

Kungiyoyin sun ce tallafa wa yara na da matuƙar muhimmaci wajen samar musu kariyar da ake da niyyar yi don inganta rayuwarsu na tsawon lokaci.

Ana ba da su a matsayin tsabar kuɗi ko kuɗin haraji, sannan tallafin yara yana da muhimmaci wajen rage talauci da kuma ba da damar kula da lafiya da samar da abinci mai gina jiki tare da samar da ingantaccen ilimi da ruwa mai tsafta.

Kazalika tallafin na taimaka wa wajen samar da ci gaban al’umma ta fuskar tattalin arziki, musamman a lokutan rikici.

Yara da dama sun gaza samun abubuwanan da suke buƙata na yau da kullum don kauce wa talauci don haka suke fuskantar barazanar tasirin da yunwa ke haifarwa da rashin samun abinci mai gina jiki da kuma gaza kaiwa wani mataki na rayuwa.

Bayanan sun yi nuni da cewa a tsawon shekaru 14 an samu matsakaicin kari a tallafin da yara suke samu a duniya, daga kashi 20 cikin ɗari a shekarar 2009 zuwa kashi 28.1 a 2023.

Adadin ɗaukar bayanan yaran da ke ƙasashe wadanda ke fama da matsalar sauyin yanayi na ƙasa sosai idan aka kwatanta da ƙasashen da ba a sanya su a matsayin wadanda ke cikin haɗari ba.

Tabbatar da cewa yara sun samu kariyar zamantakewa ta al’umma shi ne mabuɗin kare su daga duk wani tasirin mummunan tashin hankali na sauyin yanayi, a cewar ƙungiyar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like