No menu items!

Sample Page Title

Date:

Lura da yadda matsalar tsaro ke neman zama ruwan dare a sassan Najeriya, hukumomin Abuja sun bayyana yankunan Bwari da Kuje da kuma Abaji a matsayin mafiya haɗari wajen rayuwar jama’a saboda yawaitar satar mutane ana garkuwa da su.

Ma’aikatar dake kula da Abujan tace duk wasu manya manyan garkuwa da mutanen da aka gani a Abuja sun fito ne daga waɗannan yankuna, duk da yake akan samu wasu a wasu yankuna na daban.

Daraktar kula da mulki da kuma kuɗaɗe na ma’aikatar babban birnin tarayyar, Ebele Molokwu ce ta sanar da haka lokacin da take ganawa da manema labarai domin karin bayani akan ayyukan da sashen ta ya gudanar a wannan shekara.

KU KUMA KARANTA: An yi garkuwa da wasu matan aure 8 a gona a Abuja

Molokwu tace yankin Abuja ya yi iyaka da wasu jihohi da matsalar tayi ƙamari, wanda hakan kan bai wa masu aikata wannan laifi damar kutsa kai Abuja suna satar mutane lokaci zuwa lokaci.

Jami’ar tace suna ɗaukar matakai wajen amfani da dabarun zamani domin tinkarar matsalar wajen ganin sun daƙile ta, saboda muhimmancin birnin Abuja da kewaye, da kuma yawan mutanen dake zama a ciki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...