No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumomi a ƙasar Saudiyya sun shawarci mahajjata da su yi sallar Juma’a a masallatai mafi kusa, saboda yanayin zafi a ƙasar.

Hukumar kula da yanayi ta ƙasar Saudiyya, (SAMA), a ranar Alhamis ta bayyana cewa yanayi zai kai maki 50 a ranar Juma’a 7 ga watan Yuli.

Dokta Ibrahim Sodangi, kodinetan Makkah na Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

“Saboda haka, gwamnatin Saudiyya ta shawarci alhazai da su gudanar da Sallar Juma’a a masallatan da ke kusa da su domin kada su shiga cikin yanayi mai tsanani.

“Don haka an umurci Alhazan Najeriya da su bi wannan umarni,” in ji Sodangi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...