‘Yan ta’adda suna samun mafaka a makarantu a Barkin-Ladi tsawon shekaru — Gwamnan Filato

Gwamnan Jihar Filato Caleb Mutfwang ya koka kan cewa ƴan ta’adda sun shafe shekara biyar suna mamaye makarantu a ƙaramar hukumar Barkin-Ladi ba tare da an tarwatsa su ba.

Gwamnan, wanda ya faɗi hakan a cikin shirin gidan talabijin na Channels, Sunrise Daily , ya ce rikice-rikicen da ake fama da su a jiharsa na ta’azzara ne saboda jami’an tsaro ba sa yin wani kame kan lamarin.

“Daga cikin abin da ke rura wutar matsalar har da rashin yin kame ko gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu, don haka mutane na ganin kamar ana bai wa maharan kariya ne,” ya ce.

Waɗannan kalamai na Gwamna Mutfwang na zuwa ne a lokacin da aka kai wasu hare-hare kan wasu ƙauyuka da suka yi sanadin mutuwar sama da mutum 140 a ƙarshen mako, lamarin da ya tayar da hankalin al’ummar jihar.

Har yanzu ba a san waɗanda suka kai harin ba, sai dai hare-haren ƙabilanci da na rikicin makiyaya da manoma sun zama ruwan dare a jihar ta Filato.

Cikin takaici, gwamnan ya koka kan wannan sabon hari da aka kai, wanda bayan asarar rayukan da aka yi, ya kuma yi sanadin jikkatar ɗaruruwan mutane da ƙona gidaje a ƙananan hukumomin Bokkos da Barkin-Ladi.

KU KUMA KARANTA: Yawan waɗanda aka kashe a harin Jihar Filato ya kai 113

A hirar tasa ta Channels TV, gwamnan ya kuma soki gwamnatin tarayyar Nijeriya kan abin da ya ƙira “rashin son ɗaukar mataki” na kawar da ƴan ta’addar da ke cin karensu babu babbaka a jihar.

“Maganar da nake yi a yanzu, ƴan ta’adda sun mamaye makarantun ƙaramar hukumar Barkin-Ladi tsawon shekaru. An tarwatsa aƙalla al’ummomi 64 sannan waɗannan ƴan ta’addan da ke cin karensu babu babbaka sun ƙwace yankunan,” in ji gwamnan.

Gwamnan na Filato ya ce zai tuntuɓi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu don ya bai wa jami’an tsaro umarni ƙarara na kare al’ummar Filato daga maharan da ke ƙwace musu wuraren zama.

“Zan yi magana da Shugaban Ƙasa a kan wannna batun. Muna buƙatar mu samu ƙwarin gwiwar bai wa hukumomin tsaro umarnin kare mutuncin Najeriya da ma kare yankunanmu.

“Dole mu dakatar da wannan masifar, kuma bai kamata jami’an tsaro su ci gaba da bin matakan da suke ɗauka a yanzu ba, dole su ƙara ƙaimi,” a cewar gwamnan.

Shi ma shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubun ya yi tir da wadannan hare-hare tare da shan alwashin sanya hukumomin tsaro su gano masu laifin.

“Na umurci jami’an tsaronmu da su gaggauta shiga cikin wannan yankin, su karaɗe shi, tare da kamo waɗanda suka aikata wannan ta’asa.

“Bugu da ƙari, na ba da umarnin tattara kayan agaji cikin gaggawa don aika wa waɗanda suka tsira daga waɗannan munanan hare-hare, tare da tabbatar da bai wa waɗanda suka jikkata kulawar lafiya.

“Yayin da nake jajantawa gwamnati da al’ummar Jihar Filato, ina tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa, mutanen da ke jawo mutuwa da raunuka da bakin ciki ba za su kubuta daga fuskantar shari’a ba.”

A hirar tasa da Sunrise Daily, Gwamna Mutfwang ya ce yawan hare-haren da ake kai wa kan al’ummomin Filato suna da alaƙa da batun mallakar fili, inda ya ce waɗanda ba ainihin mazaunan yankin ba ne, na iya samun wajen zama a Jihar Filato salin alin ba sai ta hanyar rikici ba.

“Mutanen da ke son samun mazauni a Filato za su iya tunkarar al’ummomin da sasantawa da su. Ina ga idan aka yi hakan mutane ba za su ƙi ba, amma idan aka je musu ta salon faɗa don ƙwace musu wajen zama dole abin ya zama rikici. Ba na fatan mukai wannan matakin.”


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *