No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan sanda sun tsare Daraktan Ma’aikatar Ruwa ta Kano kan zargin karkatar da injinan rarraba ruwan sha a jihar.

Alfijir labarai ta rawaito Abubakar Gambo ya shiga hannun ’yan sanda ne tare da wasu mutane biyu kan zargin su da yin takardun bogi na smaun izinin yi gwanjon wasu manyan injinan rarraba ruwan sha da kuma tankuna.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Hussaini Muhammad Gumel, ya ce mutanen sun shiga hannun ne bayan Kwamishinan Ruwa na jihar, Ali Makoda, ya musanta ba da izinin sayar da injinna ruwan da kuma tankuna, yana mai cewa tsantar damfara ce suka shirya.

CP ya ƙara da cewa rundunarsa na ci gaba da bincike kan lamarin domin gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban ƙuliya.

KU KUMA KARANTA: Kwamishinan ‘yan sandan Kano ya bada umarnin kamo sufeton da ya harbi mutane uku a Kurna

Sauran waɗanda aka kama su ne Mataimakin Sakataren Gudanarwa, Baba Yahaya da kuma Nuhu Mansir, wanda tsohon Manajna Shirin Noman Rani a  KAREFA ne a ƙaramar hukumar Tudun Wada.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...