No menu items!

Sample Page Title

Date:

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sha alwashin magance tashe-tashen hankula yayin zanga-zangar gama garin da ake shirin gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta mai kamawa.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta fitar a yau Juma’a tace, rundunar ta tura jami’anta dubu 4 da 200 domin shawo kan duk wani nau’in tashin hankalin da ka iya tasowa yayin zanga-zangar.

Manufar tura ‘yan sandan ita ce tabbatar da tsaron al’umma da ba da kariya ga masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA:Ba za mu bari a wargaza ƙasa ta hanyar zanga-zanga ba – Rundunar Sojin Najeriya

Da ya ke tabbatar da hakkin mazauna birnin na gudanar da zanga-zanga, kwamishinan ‘yan sanda Abuja, Benneth Igweh, ya ba da shawarar cewa kamata ya yi a yi ta cikin lumana.

Ya ce, “kwamishinan ‘yan sanda ya sha alwashin daƙile dukkanin wani nau’i na tashin hankali da rashin bin doka da oda, kasancewar ‘yan sanda ba zasu kyalle suna kallo a lalata dukiyoyin hukuma da na daidaikun mutane ko kuma a samu asarar rayuka ba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...