No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ta ce ta kama wani mutum mai suna Abubakar Musa mai shekaru 43 da haihuwa da laifin mutuwar matarsa Ammi Mamman a Damaturu.

DSP Dungus Abdulkarim, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a Damaturu ranar Juma’a, inda ya ce lamarin ya afku ne a unguwar New Bra-Bra Estate da misalin karfe 4:48 na safiyar ranar Alhamis.

Abdulkarim ya ce wanda ake zargin suna kan gado ɗaya da matar ne a lokacin da aka caka mata wani abu a wuyanta, wanda ya yi sanadin zubar da jini mai yawa wanda ya kai ga mutuwarta.

KU KUMA KARANTA: An kashe wani mutum da rana tsaka a gaban iyalinsa a Kebbi

Ya ce jami’an tsaro na ‘yan sanda suna yi wa mutumin tambayoyi domin bayyana al’amuran da suka shafi mutuwar matarsa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya yi ƙira ga duk wanda ke da sahihin bayani kan lamarin da ya fito domin tabbatar da adalci ga wanda ake zargi da kuma wacce ta rasu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...