‘Yan sanda sun kama mutumin da ya kashe tsohuwar matarsa, saboda za ta sake yin aure

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta cafke wani magidanci mai shekaru 56 da laifin lakaɗawa tsohuwar matarsa ​​mai shekaru 38 dukan tsiya, ta mutu har Lahira a lokacin da ya samu labarin za ta sake yin aure washegari.

Wanda ake zargi da kisan kai mai suna Aminu Abubakar, mazaunin Lelewaji, Shagari Estate a ƙaramar hukumar Yola ta Kudu, an bayyana cewa ya fuskanci Nana Faɗimatu da misalin ƙarfe 10 na daren Juma’a da bayanin cewa za ta yi aure.

Labarun Fombina sun gano cewa ma’auratan sun yi aure shekara tara suna da yaro ɗaya kafin su rabu.

Ya fusata ya fara dukanta da wani abu mai kauri. Ta faɗi a sume ta mutu daga baya.

KU KUMA KARANTA: Matashi ya kashe mahaifiyarsa a Kano

Lokacin da angonta, Mahmud Rufa’i, mazaunin Shagari Annex, a ƙaramar hukumar, ya samu labarin faruwar lamarin, ya kai ƙararsa ga ‘yan sanda da ke ofishin ‘yan sanda na Shagari.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, SP Sulaiman Nguroje ya fitar, ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar Adamawa Afolabi Babatola ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *