Connect with us

Labarai

‘Yan sanda sun kama mutanen da ke da hannu a harin Filato

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta kama mutum uku da ke cikin wani gungun masu ɗauke da bindigogi da ya kai hare-hare a jihar Filato a jajibirin Kirsimeti waɗanda suka yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 200.

A wata sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan ƙasar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar ranar Talata da maraice, ya ce mutanen na cikin mutum 67 da suka kama bisa zargin aikata laifuka daban-daban a faɗin ƙasar.

“Mutanen da ake zargin su ne Ahmed Sulaimon da Balikisu Aliyu da Aboki Samuel. Bayan an kama su, an gano makamai da suka haɗa da bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya da ƙirar AK-49 guda ɗaya da harsasai 1000 da kwanson harsasai biyar,” in ji Adejobi.

Ya ƙara da cewa “a halin da ake ciki mutanen suna tsare a hannun ‘yan sanda kuma suna taimakawa wurin bincike.

KU KUMA KARANTA: An kafa wata rundunar tsaro ta musamman a jihar Filato

Wasu ‘yan bindiga ne suka ƙaddamar da jerin hare-hare a ƙauyuka kusan ashirin a jihar ta Filato a jajibirin Kirsimeti.

Tun da fari, hukumomi sun ce mutum 163 ne suka mutu a hare-haren da aka kai a ƙananan hukumomin Barkin Ladi da Bokkos.

Sai dai yayin da mataimakin shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya kai ziyara a jihar ta Filato, shugaban ƙaramar hukumar Bokkos Monday Kassah ya ce mutum 148 aka kashe a yankinsa.

Kazalika an kashe mutum aƙalla 50 a ƙauyuka daban-daban na ƙaramar hukumar Barkin Ladi, a cewar Dickson Chollom, wani ɗan majalisar dokokin jihar daga yankin.

“Muna rokonku da ku guji raba kawuna da kiyayya ga junanku, a yayin da muke kokarin ganin an yi adalci domin samar da zaman lafiya,” in ji Kashim Shettima a yayin da ya gana da jami’an gwamnati da sarakuna da kuma mazauna yankunan.

Olumuyiwa Adejobi ya ƙara da cewa a yunƙurin rundunar ‘yan sanda na kakkaɓe aikata laifuka a faɗin ƙasar nan, sashen leƙen asiri da dabaru ya yi nasarar kama mutum “67 da ake zargi da aikata laifuka da suka haɗa da garkuwa da mutane da sayar da makamai, da fashi da makami.”

“Kazalika ‘yan sanda sun ƙwace harsasai 5,454 da kwanson harsasai 300 da ƙananan bindigogi 68 da katin cirar kuɗi na ATM 33 da sauransu,” in ji kakakin ‘yan sanda.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like