No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama mijin marigayiya Fatima Alhaji Bukar da wasu da ba a san ko su wane ne ba suka kashe ta a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

A ranar Talata ce wasu da ba a kai ga gano su ba ne suka kashe Fatima a gidanta da ke Dikechiri Bayan Gidan Dambe a Maiduguri.

Rahotanni sun ce waɗanda suka kashe matar sun ɗaure ta da igiya, inda suka rufe bakinta don gudun ka da ta yi musu ihu tare da daɓa mata wuƙa a sassa daban-daban na jikinta, wanda a ƙarshe ya yi sanadin mutuwarta.

Wata majiya a cikin iyalan ta ce an kama mijin matar mai suna Adam Alhaji Ibrahim ne a ranar talata da daddare, bayan Gwamna Babagana Umara Zulum ya umarci hukumomi da su mayar da gawarta zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri domin a faɗaɗa bincike.

KU KUMA KARANTA: An shaƙe wuyan ‘yar ɗan majalisar dokokin jihar Borno ta mutu har lahira

A baya dai kafin umarnin Gwamnan, iyalan ta sun sanya ranar Laraba da ƙarfe 2:00 na rana domin yi mata jana’iza a gidanta da ke Maiduguri.

Gwamnan ya bayar da umarnin a bincika tare da bankaɗo aika-aikar tare da gurfanar da su gaban ƙuliya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...