Connect with us

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke da ƙoƙon kai a jihar Ogun

Published

on

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke ƙoƙon kai a jihar Ogun

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke da ƙoƙon kai a jihar Ogun

Daga Muhammad Kukuri

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 da ake zargin matsafi ne ɗauke ƙoƙon kan mutum a garin Abeoluta na Jihar Ogun

Ana zargin mutumin yana shirin yin tsafi da ƙoƙon kan ne a lokacin da ’yan sanda suka kama shi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan Kenya 400 sun tafi Haiti don aikin wanzar da zaman lafiya

Kakakin ’yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta ce jami’an rundunar sun kama wanda ake zargin ne bayan da ya haka wani kabari ya sare kan gawar da ke ciki domin yin tsafi a garin Abeokua.

Odutola ta sanar a ranar Talata cewa rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.

Continue Reading

'Yansanda

’Yan sanda sun ragargaza ’yan ta’adda a Kaduna

Published

on

Yan sanda sun ragargaza ’yan ta’adda a Kaduna

Yan sanda sun yi nasarar ragargazar masu satar mutane a kauyen Kuriga da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

’Yan sandan sun hallaka biyu daga cikin ’yan ta’addar da suka ɗauki lokaci suna addabar al’ummar yankin, bayan wani ba ta kashi a tsakaninsu.

Yayin farmakin, ’yan sanda sun yi nasarar karbe muggan makamai daga hannun ’yan bindigar da ake zargin da hannunsu wurin sace daliban Makarantar Kuriga a kwanakain baya.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan , ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

KU KUMA KARANTA:‘Yan sanda sun kama wani mutum bisa zargin kashe abokinsa da sace motarsa a Kano

Ya ce, ’yan sandan sun samu wannan nasarace bayan al’ummar yankin sun kai rahoto game da harin da ’yan bindiga suka kai wa manoma a gefen kauyen Kuriga.

“Jami’an tsaron sun yi artabu da ’yan ta’addan a wani kazamin musayar wuta, inda suka yi nasarar hallaka biyu daga cikin masu ’yan bindigar.
“Jami’an sun yi nasarar kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu da alburusai kunshi 17 ,” in ji shi.

Gwamnan jihar, Sanata Uba Sani, ya yaba wa kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Ali Audu Dabigi, tare da jami’ansa, bisa kwazon da suke nunawa.

Gwamnan ya kuma buƙace da sauran jami’an tsaro a yankin da su ci gaba da bibiyar masu aikata miyagun laifuka tare da tabbatar da tarwatsa su gaba ɗaya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like