No menu items!

Sample Page Title

Date:

‘Yan sanda sun cafke wani mutum da ya yi yunƙurin cinnawa wani masallaci wuta a birnin Dresden na ƙasar Jamus da yammacin jiya Talata.

Mutumin ya zubar da fetur a gaban wani masallaci kuma ya yi ƙoƙarin cinnawa ginin wuta, in ji kakakin ‘yan sandan.

Shaidu sun ƙira lambar hukumar bayar da agajin gaggawa bayan da suka ga mutumin yana zuba man fetur a wajen masallacin, wanda a lokacin ya cika.

KU KUMA KARANTA: Yadda kaka ta cinna wa ɗanta, matar shi da jikokin ta wuta a Ondo

An kama mutumin mai shekaru 34, kuma yana ƙarƙashin binciken ‘yan sanda kan yunƙurin tada ƙayar baya.

Duk da cewa da farko ba a san dalilinsa ba, an ce wanda ake zargin ya ƙona kwafin Alƙur’ani mai girma a wani masallaci a watan Afrilu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...