No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Taraba ta ce ta kama wasu mutane 20 bisa zargin yin garkuwa da mutane a faɗin jihar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Usman ya ce, sun kama mutanen ne bayan samun bayanan sirri da samun ƙorafe-ƙorafe wajen jama’a dangane da ayyukan masu garkuwan, da suka addabi sassan jihar.

Abdullahi Usman, ya ce duka mutanen sun amsa zargin da ake yi musu.

Ya ce jami’ansu suka ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda uku da kuma wata ƙaramar bindiga harba ka ruga.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da likita a Kogi

A cewarsa, mutanen da ake zargin sun karɓi sama da naira miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa daga iyalan waɗanda suka sace wa ‘yan uwa.

“Rundunar ‘yan sandan ba ta ja da baya ba a ƙoƙarinta na ci gaba da farautar ‘yan fashi da sauran masu aikata laifuka a jihar bisa umarnin babban sufeton ‘yan sanda Kayode Egbetokun,” in ji shi.

Usman ya kuma ce rundunar ‘yan sandan ta ƙaddamar da farautar ‘yan ta’adda a wasu wuraren da suka fi zafafa ayyukansu, musamman ma a Jalingo, babban birnin jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...