‘Yan sanda a Kano sun kama ɓarayi sama da dubu

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane sama da dubu da ake zargin ‘yan ta’adda ne a wani samame da ta kai da nufin murƙushe masu laifi a faɗin jihar.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammad Gumel ya shaida wa manema labarai a ranar Litinin a Kano cewa an kama mutanen ne a cikin watanni uku da suka gabata.

Ya ce daga cikin waɗanda aka kama akwai mutane 117 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 25 da masu garkuwa da mutane 17 da ɓarayin shanu 6 da ɓarayin babura 26 da dillalan magunguna 34 da ɓarayi 28 da kuma ɓarayin babur 27.

Gumel ya ba da tabbacin cewa duk waɗanda aka kama za a gurfanar da su a gaban ƙuliya.

Kwamishinan ya ce rundunar ta yi amfani da dabarun aikin ‘yan sanda na zamani da nufin murƙushe masu laifin.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun yi artabu da gungun masu aikata laifuka, sun ƙwato bindigogin guda biyu

Dangane da barazanar masu satar waya da ‘yan daba, Gumel ya ce ‘yan sanda sun yi musu mummunar illa, wanda hakan ya rage musu barazana ga jama’a.

“A matsayina na kwamishinan ‘yan sanda, na fahimci cewa sace-sacen waya da ‘yan daba da aikata miyagun laifuka suna kawo cikas ga zaman lafiyar jama’a a cikin babban birni da wasu sassan Kano.

“Nayi sauri na ɗauki haɗin gwiwar al’umma da dabarun fasaha don magance matsalar,” in ji shi. Ya ce an kuma daƙile wasu ayyukan ta’addanci a jihar.

“Mun yi amfani da dabarun wayar da kan jama’a na zamani tare da haɗin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro, kuma muna tattaunawa da wasu da aka gano masu aikata laifuka.

“Waɗannan sun samar da sakamako mai kyau wajen magance matsalolin tsaro a jiharmu.

“Mun ƙwato bindigogi, alburusai, babura, kwamfutar tafi-da-gidanka da sauran su daga waɗanda ake zargin da aka kama a sassa daban-daban na jihar,” Gumel ya jaddada.

Ya buƙaci jama’a da su sa kai ga sahihan bayanai da za su taimaka wa rundunar wajen kama wasu masu aikata laifuka a jihar.


Comments

One response to “‘Yan sanda a Kano sun kama ɓarayi sama da dubu”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *