No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan daba sun kashe abokin ango a wurin taron ɗaurin aure

’Yan daba sun kashe wani ɗan shekara 25 a wurin taron ɗaurin auren babban abokinsa a Jihar Neja.

Matashin, mai suna Murtala Hassan, wanda shi ne babban abokin ango ya gamu da ajalinsa ne a yayin da yake rabon faɗa a wurin bikin auren a unguwar Barkin-Sale da ke garin Minna.

Shaidu sun ce matashin wanda ke sana’ar ɗinki ya rasu ne bayan an soka masa wuƙa a rikicin ƙungiyoyin ’yan daba masu gaba da juna ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na dare.

Wani mazaunin unguwar Barikin-Sale ya ce, rikicin kungiyoyin an daɗe ana yin sa, ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Nijar sun yi nasarar kashe;yan ta;adda 29

Kakakin ’yan sanda a Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin da cewa sun samu rahoton kashe matashin a lokacin da yake ƙoƙarin raba faɗan ɓata-gari.

Ya ce ’yan sanda sun je sun ɗauke gawar a wurin inda suka kama mutum guda da ake zargi, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...