Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wata mata da yaran da suka dawo daga ƙasar waje a Kwara

Published

on

An yi zargin cewa an yi garkuwa da wasu dangi guda uku da suka haɗa da matar da ‘ya’yan wani ɗan ƙasar waje da ya dawo gida a jihar Kwara.

Lamarin ya faru ne a unguwar Okanle-Fajeromi dake ƙaramar hukumar Ifelodun, a ranar Litinin da misalin ƙarfe 11:00 na dare.

An ce ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar da ke kusa da Idofian inda suka yi garkuwa da mutanen a lokacin da suke kwance a gidajensu.

An ruwaito cewa matar wani mutumi mai suna Sikiru Abiola wanda ya dawo daga ƙetare kimanin shekaru uku yana aikin noma tare da ‘ya’yansa maza biyu waɗanda suka yi garkuwa da su da ƙarfi suka tafi da su.

Olugbense na Okanle wanda shi ne Bale (shugaban al’umma), Alhaji Abdulfatai Olasunkanmi ya tabbatar da faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Bayan ya yi kwanaki a hanun masu garkuwa da mutane, an sako babban limamin Ondo

Ya ce ‘yan bindigar sun isa unguwar ne da tsakar daren ranar litinin lokacin da mutanen ƙauyen suka yi barci suka shiga gidan Alhaji Sikiru suka yi awon gaba da mutanen.

Ya ce ’yan banga a garin sun amsa ƙarar da Alhaji Sikiru Abiola ya yi.

Bale ya ce “An harbe ɗaya daga cikin ‘yan banga a ƙafa a lokacin da suke fafata rikici da masu garkuwa da mutane kuma tuni aka garzaya da su asibiti.

“Amma an ceto ɗaya daga cikin ‘yan uwa da aka sace”.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kwara, SP Ajayi Okasanmi ya tabbatar da faruwar lamarin a yau laraba.

Okasannmi ya ce, “A yau Laraba ne aka samu rahoton lamarin kuma an tura jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro domin tseratar da daji.

Okasanmi ya ƙara da cewa “Har yanzu ba a ƙubutar da mutanen da aka sace daga hannun masu garkuwa da mutane ba amma mutanen mu suna kan hanyarsu kuma muna fatan za a ceto su.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: ‘Yan bindiga sun kashe masu haƙa ma’adinai a jihar Filato | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like