Connect with us

Labarai

’Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 7 ’yan gida ɗaya a Abuja

Published

on

Harbin harsashi ya jikkata ’yan sanda biyu yayin da wasu mutum bakwai ’yan gida ɗaya suka faɗa tarkon garkuwa na wasu ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Bwari da ke Abuja.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma harbe wani mutum mai suna Alhaji wanda ya yi wa ’yan sandan jagora a ƙoƙarin tunkarar ’yan ta’addan da suka kawo wa iyalan hari.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, ’yan bindigar a baya bayan nan sun tsananta kai hare-hare a ƙauyukan da ke yankin Bwari, inda suke kashe na kashewa sannan sun yi garkuwa da wanda tsautsayi ya faɗa kansa.

Wani mazaunin Bwari mai suna Isaiah Samuel da ya zanta da wakilinmu ta wayar tarho a wannam Juma’ar, ya ce lamarin ya faru ne da safiyar ranar Laraba yayin da ’yan bindigar suka kai farmaki kan al’ummar Zuma 1 da ke Bwarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Bauchi sun bankaɗo bindigogin AK-47 da miliyan 4.5 a maɓoyar masu garkuwa da mutane

A cewarsa, ’yan bindigar sun yi dako wuri-wuri a ƙoƙarinsu na samun nasarar cimma buƙatarsu ta garkuwa da iyalan.

Ana tsakar haka ne waɗanda aka kawowa harin cikin sanɗa suka gaggauta ƙiran wani ɗan uwansu domin a kawo musu ɗauki.

Sai dai dan uwan wanda ya yi wa ’yan sandan jagora zuwa gidan ya gamu da ajalinsa nan take yayin da aka soma musayar wuta tsakanin ’yan ta’addan da jami’an tsaro.

Samuel ya ce a sanadiyyar musayar wutar ce ’yan sanda biyu suka jikkata, yayin da ’yan bindigar suka samu nasarar tserewa da waɗanda suka kawowa farmakin.

Kazalika, Samuel ya ce makamancin wannan hari ya auku yayin da a Talatar da ta gabata ’yan bindiga suka kai farmaki ƙauyen Barangoni da ke Bwari, inda suka jikkata wani ɗan bijilanti sannan suka yi awon gaba da wasu mutum uku.

Samuel ya yi ƙira ga jami’an tsaro da su kawo musu ɗauki a sakamakon yadda ta’adar garkuwa da mazauna yankin ta tsananta a baya bayan nan.

“Gaskiyar magana ita ce yankin Bwari yana cikin matsanancin yanayi, saboda a cikin makonni biyu da suka gabata, ’yan bindiga kawai zaraya suke suna kashewa da garkuwa da mutane,” a cewar Samuel.

Aminiya ta tuntuɓi mai magana da yawun ’yan sandan Abuja, SP Adeh Josephine domin jin ƙarin bayani, inda ta nemi a ba ta lokaci ta gama tattara bayanai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like