Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji tara, sun kashe biyu a Inugu

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ke aiki a layin Imo na babbar titin Inugu zuwa Fatakwal, sun yi garkuwa da wasu fasinjoji 9 da ke kan hanyar zuwa Enugu, inda suka kashe biyu tare da yi wa wasu fashi.

Waɗanda aka kashen ‘yan asalin garin Amangwo Olokoro ne a Umuahia, an ce sun tafi Enugu ne ranar Asabar don yi musu jana’iza, lokacin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari.

Da yake bayyana halin da suke ciki ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya a Umuahia a ranar Lahadi, ɗaya daga cikinsu wanda ya bayyana sunansa da Francis, ya ce an harba motar su ƙirar Sienna da bindiga a kusa da mahaɗar Arondizuogu da ke kan babbar hanyar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe masu haƙa ma’adinai a jihar Filato

Francis (ba sunansa na gaskiya ba) ya ce daga baya aka karkatar da motar daga kan titin Arondizuogu da ke Imo, inda aka kai su wata katafariyar daji mai nisa.

Ya ce: “Ban taɓa samun irin wannan yanayin a rayuwata ba. “Muna tafiya Enugu ne don yin jana’iza, lokacin da muka isa kusa da Junction Arondizuogu, sai muka ga wasu gungun ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai, suka ce mu yi mu tsaya da motocinmu.

“Ɗaya daga cikinmu da ke cikin motar ya tambaye su ‘Me ya sa kuke neman mu yi parking kuna nuna mana bindigogi, kun san ko ni wane ne?’.

“Sai wani daga cikin ‘yan iskan ya ce, ‘yanzu oga za ka tabbatar mana da wane ne kai.

“Sun umarce mu da fitowa daga cikin motar kuma suka ce mu zauna a ƙasa mu cire rigarmu da suka rufe mana idanu da su.

“Daga nan ne suka fara dukan mutumin da ya yi wannan tsokaci da adduna,” in ji Mista Francis.

Ya ce lokacin da suka shiga unguwar, mazauna garin “suna kallon mu kamar suna kallon bidiyo.

“Lokacin da muka sauƙo daga motar, shugabansu ya tambaye shi game da mutumin da ya yi tsokaci, suka nuna masa.

“Sun fito da shi, kuma da ƙyar taku uku daga gare mu, sai suka harbe shi ya mutu har lahira.

“Wani mutum da ke tare da mu, wanda ya ga abin da ya faru kuma ya yi yunƙurin tserewa an garzaya da shi, aka kuma harbe shi,” in ji Francis.

A cewarsa, sun kama gawarwakin biyu. Ya ce maharan ba su gaza 50 a maɓoyar su ba, kuma 20 daga cikinsu ɗauke da manyan makamai.

“Kuma abin da ya fi ban dariya shi ne cewa waɗannan mutane suna magana da yarenmu.

“Sun gaya mana cewa mutanen Umuahia ‘sabo ne a gare su’, sun ce ka da mu kaɗa ƙuri’a a zaɓen da ya gabata kuma mun fito zaɓe.

“Cewa sun ayyana ranar Litinin a zauna a gida kuma ba ma yi musu biyayya. “Duk mutumin Umuahia da suka samu a nan zai yi zafi.

“Sai suka nemi mu yi addu’o’inmu na ƙarshe,” in ji Francis.

Ya ce suna cikin addu’o’in ne aka shigar da su ɗaya daga cikin sabbin motocin ƙirar ‘Hummer’ guda uku da ke cikin maɓoyar sannan aka kai su inda a ƙarshe suka loda su a cikin motar su ta Sienna suka kai su hanyar da ta kwalta.

“A nan ne suka tambaye mu ko za mu iya nemo hanyarmu, muka ce a’a, sai suka ce wa direban ya miƙe.

“Sun ce mu je mu gaya wa mutanen Umuahia abin da muka gani. “Hakan ne muka samu kanmu zuwa Umuahia,” in ji shi.

Mista Francis ya ce kayayyakin da aka karɓa daga wajensu, sun haɗa da kudi da wayoyin hannu.

A halin da ake ciki dai, waɗanda suka mutun an bayyana sunayensu da Fasto Chukwuemeka Nwachukwu, wanda ya yi tsokaci bayan an ba su tuta, da kuma shugaban matasan ƙauyen, Ifeanyi Onwunkwe, wanda ya yi yunƙurin tserewa.

Wani ɗan jarida daga yankin ya ce bisa sharaɗin ɓoye sunansa cewa “al’amarin baƙin ciki ya jefa yankin cikin makoki”.

Ƙoƙarin samun tabbacin harin daga jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan Imo, ASP Henry Okoye, ya ci tura, saboda ƙiran wayar da aka yi masa ya gagara gamuwa da shi.

Sai dai wani babban jami’in ‘yan sanda a hukumar ‘yan sandan jihar Abia ya yi iƙirarin cewa yana sane da faruwar lamarin amma ya ce har yanzu ba a kai ga shiga ba.

“Ina sane da harin na ranar Asabar amma kun san lamarin ya faru ne a Imo.

“Don haka, yayin da muke magana, babu wanda ya shiga nan a hukumance,” in ji majiyar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Masu garkuwa da mutane sun kashe mata mai shekaru 60 bayan sun karɓi kuɗin fansa miliyan ɗaya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like