No menu items!

Sample Page Title

Date:

‘Yan bindiga sun sako mahaifiyar Rarara

’Yan bindiga sun sako mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasa, Dauda Abdullahi Kahutu Rarara, da suka yi garkuwa da ita.

Mawaƙin da kansane ya sanar da hakan tare da wallafa hotonsa tare da ita bayan an sako ta; kimanin kwana 20 ke nan da ’yan bindiga suka yi garkuwa da dattijuwar a gidanta da ke Karamar Hukumar Danja a Jihar Katsina.

A cikin bidiyon, an ga Rarara zaune a kusa mahaifiyar tasa, yana rungume da ita

Ya kuma bayyana bayyana godiyarsa ga Allah da ya kungiyar da mahaifiyar tasa, tare da mika godiya ga mutane da suka taimaka da addu’o’i a kan lamarin.

A ranar 28 ga watan Yuni, 2024, ’yan bindiga suka yi garkuwa da mahaifiyar Rarara, inda daga bisani suka buƙaci kuɗin fansa Naira biliyan ɗaya.
Daga baya sun rage kuɗin zuwa miliyan 900.

An yi garkuwa da Hajiya Halima  ne a ranar 28 ga watan Yuni, a gidanta da ke yankin Kahutu a Karamar Hukumar Danja ta Jihar Katsina.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Shaidu a ƙauyen sun ce da misalin karfe ɗaya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka kai harin suka yi garkuwa da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba  a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunkuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke dauke da su,” in ji wani mazaunin kauyen na Kahutu.

Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin kauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kubutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan kauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan cigaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...