No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan bindiga sun kai hari inda suka sace dalibai da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kogi (CUSTECH).

A daren Alhamis ne ’yan bindigar suka kutsa harabar jami’ar da ke yankin Osara, inda suka ɗauke ɗalibai da kawo yanzu ba a tantance adadinsu ba.

Wani ɗalibin jami’ar wanda ya tsallake rijiya da baya, mai suna John, ya shaida mana cewa “Misalin karfe 9 na dare muka fara jin ƙarar harbi a lokacin da muke cikin ɗakunan karatu saboda muna shirye-shiryen jarabawa.

“Wasunmu sun tsere, amma na san an kama wasu ɗalibai”, in ji wani ɗalibin jami’ar mai suna John.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

Rahotanni daga jami’ar sun ce ’yan banga da ke yankin sun kai ɗauki, amma maharan sun fi su ƙarfin makamai.

Zuwa wannan lokaci dai babu cikakken bayani saboda mahukunta sun ƙi cewa komai a kai, sai nan gaba.

Mun tuntuɓi kakakin ’yan sandan jihar Kogi, SP Williams Aya, amma har muka kammala rubuta wannan labarin ba mu ji daga gare shi ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...