‘Yan bindiga sun kashe wani Hakimi a jihar Neja

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe Malam Usman Sarki, hakimin garin Zazzaga da ke ƙaramar hukumar Munya a jihar Neja.

Wani shugaban al’ummar da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya cewa ‘yan bindigar sun ƙaddamar da harin ne a Zazzaga da ƙauyukan da ke maƙwabtaka da su a daren Talata, 10 ga Oktoba, 2023.

Majiyar ta ce an kuma yi garkuwa da wasu manoma da ba a tantance adadinsu ba ciki har da mata.

“An kai harin ne cikin dare ranar Talata.  Sun harbe Hakimin ƙauyen na Zazzaga, Malam Usman Sarki har lahira tare da yin garkuwa da wasu da dama,” inji majiyar.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe basarake sun ƙona gawarsa a Imo

“A yanzu, ba za mu iya bayar da ainihin adadin mutanen da suka tafi da su ba.  Sun kuma yi awon gaba da shanu da awaki da tumaki da yawa namu.”

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, DSP Wasiu Abiodun, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayani kan harin da ake zargin an kai ba.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *