Connect with us

Laifi

’Yan bindiga sun kashe kansila a Katsina

Published

on

’Yan bindigar sun kashe Samaila Buhari Mairago a yayin da yake shirin gudanar da aikin sintiri a matsayinsa na ɗaya daga cikin jami’an samar da tsaro.

Shaidu sun ce ’yan bindigar sun kashe Kansilan gundumar Nasarawa, Hon Samaila Buhari Mairago ne bayan dawowarsa daga ofishin ’yan sanda inda ya karɓo bindiga domin gudanar da sintiri a matsayinsa na ɗaya daga cikin jami’an samar da tsaro da gwamnatin jihar ta horas.

Wani maƙwabcinsa, Malam Musa Maibulo, ya ce bisa alama maharan sun shigo yankin ne da nufin sace wani, amma tsautsayi ya faɗa kan kansilan a daren na Litinin.

Malam Musa ya ce, “babu wanda ya lura, kowa na gudanar da harkokinsa ba tare da sanin cewa ɓata-garin sun shigo ba.

KU KUMA KARANTA: Ɗan ƙunar-baƙin-wake ya kashe mutane 52 a wurin Maulidi a Pakistan

“Kansilanmu Samaila Buhari wanda ke cikin masu sintiri ya je ofishin ’yan sanda na Maƙera ya ɗauko bindigarsa domin aikin sintiri yadda suka saba, amma aka yi rashin sa’a, ya je shiga gidansa, sai ’yan bindigar suka lura da bindigar da yake rataye da ita, shi ne suka buɗe masa wuta,” suka ɗauke bindigar suke tsere nan take.

Ya ce sai “bayan tserewarsu ne muka gane cewa sun sace wani maƙwabcinmu mai suna Malam Samaila Maikatako.”

Wani kawun mamacin, Abbas Isma’il wanda ya ce marigayin ya bar mace ɗaya da ’ya’ya takwas, ya ce, “Abin takaici ne yadda ’yan bindiga suka addabi garin Funtuwa.

“Ko a ranar 3 ga watan Agusta sai da suka sace wata fitacciyar mai sayar da abinci, Hajiya Fati Mai Waina, kuma har yanzu ba su sako ta ba.”

Kakakin ’yan sandan Jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce rundunar ta samu rahoton abin da ya faru kuma tana gudanar da bincike a kai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Laifi

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Published

on

'Yan bindiga sun sace 'yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Daga Idris Umar, Zariya

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ‘yan jarida biyu a ƙauyen Danhonu da ke ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kai hari a cikin al’umma a daren ranar Asabar inda suka yi awon gaba da ‘yan jarida biyu da iyalansu.

Waɗanda abin ya shafa, Alhaji AbdulGafar Alabelewe da AbdulRaheem Aodu, ‘yan jarida ne na jaridun The Nation da Blueprint a jihar Kaduna, bi da bi.

Alabelewe wanda shi ne shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), majalisar jihar Kaduna a halin yanzu, an dauke shi tare da matarsa da ‘ya’yansa biyu.

An kuma yi garkuwa da Aodu da matarsa, inda suka bar ‘yarsu da ba ta da lafiya.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

Da yake bayyana hakan, Taofeeq Olayemi, dan uwa na daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya ce ‘yan bindigar sun afkawa al’ummar ne da misalin karfe 10:30 na dare, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su yi awon gaba da su.

Da farko ‘yan fashin sun tafi da Alabelewe, matarsa, ‘ya’yansa uku, da kuma wani bako, amma daga baya suka sako yarinyar daya daga cikin yaran.

“Sun shiga gidan Abdulgafar ta katanga.

“Sun shiga cikin ɗakin kwanansa kai tsaye suka ɗauko shi da matarsa da ‘ya’yansu biyu suka tafi nan take, inda ‘yan banga suka iso suka fara harbin iska,”

Ya zuwa haɗa wannan rahoton babu ɗuriyar duk wanɗana aka sacen.

Tuni kunyar ‘yan jaridar ta jihar Kaduna ta sanar tare da tabbatar da faruwar lamarin.

Continue Reading

Laifi

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Published

on

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Ana zargin wani matashi mai suna Ufuoama Umurie ya kashe mahaifinsa a Unguwar Okpare da ke Ƙaramar Hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, ranar Laraba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, an tsinci gawar mahaifin mai suna Rabaran Isaac Umurie, wanda ɗaya ne daga cikin limaman cocin St. John’s Anglican da ke Okpare-Olomu a safiyar wannan Larabar.

Bayanai sun ce tun farko lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar dare, inda wanda ake zargin ya kori mahaifiyarsa a lokacin da take ƙoƙarin ceto rayuwar mijinta amma ita kanta da ƙyar ta tsira.

Ufuoma, wanda a halin yanzu yana hannun ‘yan sanda, an ce ya yi amfani da laujen yankar ciyawa ya yanka mahaifinsa sannan ya sassare shi a sassan jikinsa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni sun ce matashin ya yi wa mahaifinsa wannan aika-aikar ce a lokacin da yake barci kafin maƙwabta da mabiya cocin su su kawo ɗauki.

Duk da cewa har yanzu ba a gano abin da ya haddasa faruwar lamarin ba, wasu mazauna unguwar yankin sun yi zargin cewa Ufuoma yana fama da taɓin hankali, kuma wannan ne karo na biyu da ya kai wa mahaifin nasa hari.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like