Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun kashe fastoci 23, sun rufe coci sama da 200 a Kaduna – Ƙungiyar CAN

Published

on

Shugaban ƙungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) reshen jihar Kaduna, Joseph Hayab, ya ce ‘yan bindiga sun kashe fastoci 23 tare da rufe coci sama da 200 a faɗin jihar Kaduna.

Mista Hayab ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da kwamishinan ‘yan sandan jihar, Musa Garba, da limaman coci-coci daban-daban na ƙananan hukumomi 23 na jihar.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa cocin ya shiga mawuyacin hali sakamakon ayyukan masu aikata laifuka a jihar.

Ya ce: “Wani Fasto da aka yi garkuwa da shi a ranar 8 ga Agusta 2023, ya shaida wa shugabannin CAN cewa akwai Kiristoci sama da 215 da ‘yan bindigar suka sace a dajin Birnin Gwari.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Kebbi sun kashe mutane biyu, sun sace mutane bakwai

“Har yanzu suna nan kuma Fasto ya shaida mana cewa ‘yan bindigar sun nemi ya yi addu’a ga Kiristoci 215 a lokacin da yake cikin kogon su.

“Muna ƙira ga Kwamishinan ‘yan sanda, da ya duba wannan batu a tsakanin sauran mutane gaba ɗaya don ƙara ƙarfafa ƙwarin gwiwar jama’a,” in ji Mista Hayab.

Shima da yake jawabi, tsohon babban sakataren ƙungiyar Evangelical Church Winning All, (ECWA), a faɗin duniya, Yunusa Nmadu, da sauran limaman cocin da suka yi jawabi a wurin taron sun buƙaci kwamishinan ‘yan sandan ya kuma yi la’akari da kamo limamai da suka tsunduma cikin wa’azin ƙiyayya da kalaman ƙiyayya.

Limaman sun yi ƙira ga kwamishinan ‘yan sanda da ya duba lamarin masu sayar da miyagun ƙwayoyi, inda suka ce galibin laifukan ana aikata su ne ta hanyar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Da yake mayar da martani, kwamishinan ‘yan sandan, ya jaddada cewa aikata laifuka ba shi da addini, yana mai cewa duk wanda ya aikata wani laifi to a ƙira shi a matsayin mai laifi ba tare da bayyana shi a matsayin Kirista ko Musulmi ba.

“Tsaro alhakin kowa ne ba na gwamnati kaɗai ba. Yayin da gwamnati ke kan gaba wajen kare rayuka da dukiyoyi, ana kuma sa ran ɗaiɗaikun mutane za su taka rawar gani musamman a fannin samar da bayanai.

“Taron ya kasance don ƙarfafa dangantakar da ke tsakanin ‘yan sanda da shugabannin addini da sauraron ƙalubalen da suke fuskanta tare da samar da hanyoyin da za a iya magance su.

“Rundunar ‘yan sanda ƙarƙashin jagorancina a jihar za ta yi iya ƙoƙarinta wajen gudanar da ayyukanmu. Ya kamata mu zama masu kiyaye ’yan’uwanmu.

“Koyaushe ku tuntuɓi jami’an tsaro da ke kewaye da al’ummomin ku da bayanan gaggawa da zarar kun gano mutanen da ake tuhuma,” kwamishinan ya umarci limaman.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: ‘Yan bindiga sun kashe mutane huɗu, sun sace 18 a Sakkwato | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like