No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mahara sun kai farmaki kan jama’a a kasuwar Didango da ke ƙaramar Karim Lamiɗo da ke Jihar Taraba.

Wani mazaunin garin, Yakubu Adamu ya shaida wa manema labarai cewa mahara kusan 200 ɗauke da makamai ne suka far wa kasuwar a ranar Laraba, suka kashe mutum biyu, suka jikkata wasu da dama sannan suka wawushe kayayyaki na miliyoyin Naira.

Ya ce a yayin da kasuwar ke tsaka da ci a ranar Laraba ne maharan, waɗanda ake zargin ’yan sa kan wata ƙabila ce, suka far mata bagatatan, “ba tare da an tsokane su ba suka far wa Didango, wanda yawancin mazaunansa Fulani, Hausawa, Jarawa da kuma ’yan ƙabilar Wurkum ne.

Sai dai ya ce matasan Didango sun yi arangama da maharan suka fatattake su, a yayin da wata majiya ta yi zargin an kawo musu harin ne domin tayar da rikicin ƙabilanci a yankin.

Kakakin ’yan sandan Jihar Taraba, SP USman Abdullahi ya tabbatar da harin, amma ya ce mutum ɗaya ne aka kashe.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...