No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’ar Jihar Filato, (PLASU), ta ce jami’an tsaronta sun daƙile wani hari da ‘yan bindiga suka kai harabar jami’ar a daren ranar Talata.

Hukumar makarantar ta ce wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan kwanan ɗaliban makarantar da ke Bokkos tsakanin daren Talata zuwa Laraba amma ba a yi garkuwa da su ba.

John Agams, jami’in hulɗa da jama’a na jami’ar ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Najeriya aukuwar lamarin. Mista Agams ya ce masu laifin sun kai hari makarantar ne domin yin garkuwa da ɗalibai amma jami’an tsaro na jami’ar sun daƙile su.

“Gaskiya ne ‘yan bindiga sun yi yunƙurin sace wasu ɗalibanmu, amma jami’an tsaron mu na yankin sun daƙile yunƙurin. “A cikin haka, ɗalibi ɗaya ya samu rauni, amma babu wani ɗalibi da aka sace.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace mahaifin ɗan majalisa a Zamfara

“A halin yanzu mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Benard Matur yana harabar makarantar kuma yana ƙira ga ɗalibai da su kasance cikin lumana,” inji shi. Sai dai har yanzu rundunar ‘yan sandan jihar ba ta ce uffan ba kan lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...