Connect with us

'Yan bindiga

’Yan bindiga sun dawo hanyar Abuja-Kaduna, sun sace matafiya 30

Published

on

Lamarin ya faru ne ranar Lahadi a Dogon-Fili kusa da Katari a ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Karo na farko ke nan cikin fiye da wata 10 da mahara suka sace jama’a a kan titin Abuja zuwa Kaduna.

Binciken Aminiya ya nuna cewa hari na karshe da aka kai a kan titin shi ne na ranar 1 ga watan Maris, 2023, wanda da aka sace mutum 23.

Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya sanar a shafinsa na X cewa abokansa biyu daga ’yan siyasa sun tsallake rijiya da baya a harin na ranar Lahadi.

Ya ce ’yan bindigar sun ci karensu babu babbaka na tsawon lokaci duk da cewa an girke jami’an tsaro a kan babar hanyar.

Shehu Sani ya ce, “A daidai lokacin da muke tunanin mun samu kwanciyar hankali, a daren jiya (Lahadi) ’yan bindiga sun kai hari, sun dawo hanyar Kaduna-Abuja.

“Sun tare hanyar da misalin karfe 9 na dare inda suka sace mutane masu yawa a kusa da ƙauyen Katari.

“Abokaina biyu, ɗan jam’iyya mai mulki da ɗan adawa sun tsere daji kamar Usain Bolt.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun kashe ɗan uwan amarya, sun sace mahalarta biki a Kaduna

“Amma duk da an inganta tsaro a kan hanyar fiye da yadda yake a baya.”

Wani mazaunin Katari, Suleiman Dan Baba, ya ce da misalin ƙarfe 9:33 na dare ne ’yan bindiga ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47 suka fito daga daji suka tare kowane ɓangaren titin kuma sun ɗauki tsawon minti 45 a kan hanyar.

Suleiman ya ce maharan sun buɗe wa motocin matafiya wuta, suka fasa musu tayoyi, wanda hakan ya sa dole suka tsaya.

“’Yan bindigar sun tilasta wa matafiya fita daga motocinsu da bakin bindiga, suka wuce da su cikin daji,” in ji shi.

Wani mazaunin garin Jere, Samaila Shehu, ya ce lamarin ya faru ne da nisan kimanin kilomita daya daga garinsu, kuma an sace matafiya sama da 30 a wurin.

‘Yan bindigar sun raba kan su gida biyu, inda ɗaya tsagin suka kai farmaki ƙauyukan Bishini da Kokore da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, ɗaya tsagin kuma suka yi awon gaba da matafiya da ba a tantance adadinsu ba.

Wani shugaba a yankin Jere, Shu’aibu Adamu Jere, shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa ɗan uwansa ya kuɓuta daga harin na kusa da Katari a ranar Lahadi.

Ya ce an jikkata wani direba, sannan an gano motoci biyu, ƙirar Sharon da wata ƙaramar mota a bakin hanya babu kowa a cikinsu bayan harin.

“Eh, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:30 na dare, kuma sun dauki tsawon minti 45 a kusa da Dogon Fili da ke kusa da Katari a ranar Lahadi.

“An harbi wani direban ɗaya daga cikin motocin kuma aka bar shi a wurin. Akwai wani ɗan uwana da ya tsira daga harin,” in ji shi.

Sai dai ya kasa bayyana adadin mutanen da aka sace a harin, amma ya ce an garzaya da direban da ya jikkata zuwa wani asibiti da ba a bayyana ba domin yi masa magani.

Shi ma wani mazaunin Katari, wanda lauya ne amma ya buƙaci a sakaya sunansa, ya tabbatar da cewa an tare hanyar a daren Lahadi a lokacin da yake shirin komawa Kaduna.

A cewarsa, sojojin da ke da nisan mil 500 daga Katari sun fatattaki ’yan bindigar.

“An faɗa min cewa ’yan bindiga sun tare hanya a daren kafin sojoji da ke Katari su zo zu fatattake su. Amma ban sani ba ko an sace mutane,” in ji shi.

Da aka tuntuɓi kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya ce ba zai iya tabbatar da faruwar lamarin ba.

Shi ma kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Mansir Hassan, da aka tuntube shi, ya ce zai bincika dom tabbatar da gaskiyar lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

'Yan bindiga

An sace limaman coci 6 a Anambara

Published

on

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu limaman Coci shida yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa birnin Awka na jihar Anambara a kudu maso gabashin Najeriya.

Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan bindigar sun sace Archbishop Uka Uka na Mujami’ar Brotherhood of the Cross and Star, (BCS) da matarsa Anne Osim da ɗansu Ronald Uka Osim.

Sauran limaman Cocin sun haɗa da Azuka Ochu, Moses Okafor da Anderson Akwazie a cewar jaridar Daily Trust.

Jaridar Daily Post ta yanar gizo ta ruwaito cewa mutanen na hanyarsu ta zuwa Awka ne daga jihar Abiya don gudanar da ayyukan wa’azi a lokacin da lamarin ya faru.

Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna.

KU KUMA KARANTA:An halaka direba da sace mutum 2 a hanyar Abuja

“Mun damu matuƙa, amma muna da tabbacin cewa Ubangijin da suke bautawa zai taimaka musu.” Jaridar ta Daily Post ta ruwaito wani Limami a Cocin ta BCS, Bishop Denis Onuoha yana cewa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Anambara, ta ce ba ta da masaniyar aukuwar wannan al’amari.

“Ba mu da wasu bayanai da suka nuna aukuwar wannan al’amari a jihar Anambara.” Wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce a ranar Asabar ɗauke da sa hannun Kakakinta SP Tochukwu Ikenga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “muna ƙira ga jama’a da su taimaka mana da bayanai kan wannan al’amari idan har ya faru, hakan zai ba mu dama mu ƙaddamar da bincike.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like