No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani mummunan lamari ya auku a jihar Imo yayin da Jaridar Vanguard ta rawaito cewa ‘yan bindiga sun kashe soji takwas, ‘yan sanda da jami’an NSCDC a wani ƙazamin kwanton ɓauna da suka yi masu.

Vanguard ta rawaito a ranar Talata ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba, suka kai hari tare da kashe jami’an tsaro a ƙalla takwas, tare da ƙona motoci biyu a jihar Imo.

Wani ganau ya shaida wa manema labarai cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na safe a Oriagu, daura da reshen Aba da ke ƙaramar hukumar Ehime Mbano a jihar Imo.

Jami’an tsaron da abin ya shafa dai sun haɗa da sojoji da ‘yan sanda da kuma jami’an tsaron farin kaya na Najeriya, NSCDC.

Bidiyon harin da aka kai, ya nuna gawarwakin sojoji kusan huɗu waɗanda ba su da rai a cikin kakinsu da bindigogi.

Haka kuma motocinsu guda biyu suna ci da wuta.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe basarake sun ƙona gawarsa a Imo

A lokacin da ake gabatar da wannan rahoto, an ce an ba da kariya ga titin da ta isa wurin da lamarin ya faru.

Tashin hankali ya ci gaba da gudana a ciki da wajen al’ummar da abin ya shafa.

A cewar ganau, “Al’amarin ya faru ne kimanin sa’o’i biyu da suka wuce.  Da farko na ga motocin Hilux guda biyu a lokacin da suka taso daga Oriagu sun nufi reshen Aba da ke Ehime Mbano.

“Kamar yadda nake magana da ku yanzu motocin Hilux na ci gaba da cin wuta ‘yan bindigar sun ƙona sojojin.

“Tashin hankali yana ko’ina.  Mun rufe shagunanmu, mu je gida, muna ganin jami’an tsaro da yawa, sun tare hanya, mutane suna gudu zuwa gidajensu jama’ar mu na fargabar komai na iya faruwa a yanzu.

“Motar farko, na ga sojoji sama da biyar.  A na biyu kuma na ga jami’an tsaro sama da huɗu.  Sun ce an kashe su duka.”

Har ya zuwa lokacin miƙa wannan rahoton, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Imo, PPRO, Henry Okoye, bai mayar da martani kan binciken ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...