No menu items!

Sample Page Title

Date:

‘Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

Daga Ali Sanni

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun ƙona gidaje 23 a yankin Egwuma da ke ƙaramar hukumar Agatu dake jihar Binuwai.

Mazauna yankin sun bayyana cewa mutane da dama sun tsallake rijiya da baya a harin wasu kuma da raunukan harbin bindiga.

Shugaban ƙaramar hukumar Gari, Philip Ebenyakwu, ya shaida wa manema labarai a Makurɗi, babban birnin jihar, cewa mutane uku ne suka tsira da raunukan harbi.

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan ‘Boko Haram’ a Borno sun kashe ɗan sanda da ƙona motocin sintiri

Ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, kuma waɗanda aka ji wa raunukan suna samun kulawa a asibiti.

Ya ce, “Makiyaya ɗauke da makamai daga jihar Kogi suna yawan kai hare-hare a Agatu ta yamma.

“Yankin da aka kai wa hari yana iyaka da jahar Kogi, kuma yana yawan fuskantar barazana.

“Ranar lahadi makiyayan suka kai hari a yankin Egwuma, inda suka ƙona gidaje 23 suka sace babura biyu.”

Duk da haka, Ebenyakwu, ya yaba wa jami’an tsaron da aka tura yankin.

Ya bayyana cewa a ranar Asabar wani sojan ruwa ya ƙwace jirgin ruwa da ’yan bindiga ke shigowa a kai daga jihar Nasarawa.

Wakilinmu yayi ƙokarin tattaunawa da kakakin ‘yan sandar jihar ta Binuwai, SP Catherine Anene, amma hakan baiyuba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...