’Yan banga sun kashe ’yan bindiga a Kebbi

0
198

’Yan banga sun hallaka wasu ’yan bindiga uku suka addabi yankin Ngaski da ke jihar Kebbi da satar mutane.

’Yan bindigar sun gamu da ajalinsu a hannun ’yan banga ne a maɓoyarsu da ke ƙaramar hukumar Ngaski ranar Alhamis.

Masu garkuwa da mutanen sun jima da addabar yankin kafin dubunsu ta cika bayan ’yan banga sun fara cafke masu yi musu leƙen asiri.

Darektan tsaro na jihar, AbdulRahman Usman ya ce “bayan kama masu yi wa ’yan bindigar leƙen asiri ne suka jagoranci ’yan banga zuwa maɓoyarsu da ke cikin jeji, inda aka yi musayar wuta da su,” suka ci ƙarfinsu.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano

Ya bayyana jin daɗinsa bisa nasarar da ’yan bangar suka samu ba tare da asarar rai ko rauni ba.

Ya kuma jinjina musu game da yadda suke taimaka wa hukumomin tsaro wajen magance matsalar tsaro a jihar.

Leave a Reply