Connect with us

Labarai

’Yan acaɓa sun kai hari ofishin ’yan sanda a Legas

Published

on

’Yan acaɓa sun kai hari ofishin ’yan sanda a Legas

’Yan acaɓa sun kai hari ofishin ’yan sanda a Legas

Wasu ’yan acaba ɗauke da muggan makamai sun kai farmaki ofishin ’yan sanda na yankin Ipaja da ke Jihar Legas a safiyar ranar Litinin.

Farmakin ya sa ’yan sandan yin artabu da ’yan acaɓar da suka kai hari ofishin.
Lamarin dai ya haifar da firgici da ruɗani a tsakanin mazauna yankin, lamarin da ya sa aka aike ƙarin jami’an ‘yan sanda don tabbatar da tsaro.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Legas, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta shawo kan lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“Jami’an ’yan sandan yankin Ipaja sun yi nasarar daƙile wani hari da wasu ‘yan acaɓa suka kai musu a safiyar yau.

“Harin na zuwa ne bayan da jami’an ’yan sanda suka hana yin sana’ar acaɓa a Jihar Legas.

“Maharan waɗanda suka yi dandazo, sun afka wa ofishin ‘yan sandan yankin da muggan makamai, inda suka yi ƙoƙarin ƙwace ofishin. Sai dai jami’an ofishin sun yi artabu da su, har zuwa lokacin da aike musu ƙarin tawaga.

“Biyu daga cikin maharan sun samu munanan raunuka yayin harin. An yi nasarar cafke wasu daga cikin maharan.

“Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na tabbatar da doka da oda a tsakanin al’umma,” in ji Hundeyin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Published

on

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Ministan Harkokin Noma na Najeriya Mohammad Abubakar ya ce Saudiyya ta nuna sha’awar fara shigar da ton 200,000 na naman shanu da ton miliyan ɗaya na waken suya cikin ƙasarta duk shekara daga Najeriya.

Minista Mohammed ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis a Abuja cewa Saudiyya ta nuna sha’awar hakan ne bayan da Ministanta na Harkokin Noma ya ziyarci Najeriya tare da yin wasu taruka da ‘yan kasuwa a fannonin noma.

“Nuna sha’awar tasu kan wannan batu ke da wuya sai muka fitar da wani tsari da za mu iya samar da yawan abin da suke so da kuma biya musu buƙatarsu,” a cewar Ministan Harkokin Noman na Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Masu sana’ar sayar da tumatur sun yi barazanar daina kai wa jihar Legas

Ya ƙara da cewa dama Najeriya na neman abokan hulɗa na kasuwanci don samun kuɗaɗen ƙasashen waje bayan da ta sha fama da ƙarancin dalar Amurka, lamarin da ya yi mummunar illa kan tattalin arzikinta da kuma rage darajar kudin ƙasar na Naira sosai.

Najeriya ta daɗe tana son raba ƙafa kan harkokin fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje, maimakon fitar da ɗanyen man fetur kawai, wanda a yanzu fitar da shi shi kaɗai ba ya iya riƙe tattalin arzikinta sosai.

Continue Reading

Labarai

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Published

on

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Daga Muhammad Kukuri

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya ɗaga tutar mulki a ƙaramar fadar da ke unguwar Nassarawa inda yake zaune.

A bisa al’ada, tutar na zama ne a matsayin alamar iko, kuma daga ta na alamta cewa sarki yana cikin fada.

Wannan kuwa na zuwa ne duk da umarnin gwamnatin Kano ga Sarki Aminu ya fice daga fadar a yayin da ake ci gaba da dambarwar sarautar Kano.

Akan daga tutar ce da misalin karfe 6 na safe a kuma sauke ta 6 na yamma ko idan sarki ya yi bulaguron aiki.

Neptune Prime Hausa ta gano cewa ba a ɗaga tutar ba a Fadar Nassarawa ba sai a safiyar Alhamis, duk da cewa an sanya karfenta a safiyar Laraba.

An yi ta ji-ta-ji-ta ranar Laraba cewa an sanya tutar, amma mun gano cewa kafen kawai aka sa, Alhamis da safe kuma aka daga tutar.

Daga tutar a karamar Fadar Nassarawa na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da shari’ar da Gwamnatin Kano ke neman kotu ta hana Aminu Ado Bayero Aminu gabatar da kansa a matsayin Sarkin Kano bayan ta maye gurbinsa sa Muhammadu Sanuni II, Sarkin Kano na 16.

Gwamnatin jihar ta je kotu ne tana neman a hana duk sarakuna biyar da ta rushe masarautunsu a jihar gabatar da kansu a matsayin sarakunan masarautun.

Continue Reading

Labarai

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Published

on

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Daga Muhammad Kukuri

Majalisar Wakilai ta amince da buƙatar ci gaba da aiwatar da kasafin ƙuɗin 2023 har zuwa ƙarshen shekarar 2024.

Hakan dai na kunshe ne cikin ata sanarwa da majalisar ta fitar ta hannun shugaban kwamitin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Akin Rotimi.

Ya bayyana cewa, “an amince da ƙudurin ne domin amfanin ƙasa baki ɗaya, bayan zazzafar muhawara da aka tafka kan lamarin.”

Sanarwar ta ce “Majalisar wakilai ta amince da dokoki biyu waɗanda suka buƙaci tsawaita aiwatar da kasafin kuɗi na 2023 da kuma ƙaramin kasafin kuɗi na shekarar ta 2023 har zuwa watan Disamban 2024.”

KU KUMA KARANTA: El-Rufai ya kai ƙarar Majalisar Dokokin Kaduna kotu

Ana iya tuna cewa dai Shugaba Bola Tinubu ne ya tura ƙudurorin biyu zuwa majalisar dokoki.

A lokacin muhawara kan ƙudurorin, wasu ’an majalisa sun nuna shakku game da buƙatar amincewa da su cikin sauri, inda suka yi fargabar kada ya kasance akwai wani abu da zai cuci al’ummar ƙasa.

Daga cikin waɗanda a farko suka yi tirjiya kan aiwatar da ƙudirin har da shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda da tsohon bulaliyar majalisar, Alhassan Ado Doguwa.

Sai dai bayan tattaunawa da kuma duba ɓangarorin dokar a matakin kwamiti, zauren majalisar ya sake zama inda ya amince da ƙudurorin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like