No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya sun ba da sanarwar shiga yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar Talata 3 ga watan Oktoba a faɗin ƙasar.

Ƙungiyoyin NLC da TUC sun bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai na haɗin gwiwa da suka ƙira da yammacin ranar Talata a babban birnin ƙasar, Abuja.

Sun buƙaci rassansu na jihohi su harhaɗo kan ‘yan ƙwadago da sauran jama’a don gudanar da jerin zanga-zanga a faɗin Najeriya.

Kafofin yaɗa labarai a Najeriya na cewa sun fahimci cewa shugabannin ƙungiyoyin ƙwadagon biyu sun warware bambance-bambancen da suka sanya ƙungiyar NLC shiga wani yajin aikin gargaɗi tsawon kwana biyu, ba tare da takwararsu ta TUC ba.

NLC ta ƙaurace wa aiki a ranakun 5 da kuma 6 ga watan Satumba da muke ciki don matsa lamba ga gwamnatin ƙasar a kan ta shawo kan wahalhalun da ‘yan Najeriya, musamman ma’aikata ke ciki, sakamakon cire tallafin man fetur.

KU KUMA KARANTA: Katsewar wutar lantarki sakamakon yajin aikin gargaɗin NLC – AEDC

A cewar sanarwar da sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja ya fitar, ƙungiyoyin na gudanar da taron ne ta intanet.

A lokaci guda kuma, ministan ƙwadago, Mista Simon Lalong ya roƙi shugabannin NLC su dakatar da shirinsu na tafiya yajin aikin, inda ya ba su tabbacin cewa gwamnati na nan a kan ƙudurin magance damuwar da suka bijiro da ita.

Ministan, kamar yadda tashar Channels TV ta ruwaito, ya kuma nunar da cewa ɗaya daga cikin manyan buƙatun NLC a taron da suka yi na baya, tuni an cimma ta, inda ta ba da umarnin sakin shugaban ƙungiyar ma’aikatan sufurin mota a ƙasar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...