Connect with us

'Yansanda

Yadda ‘yan yahoo suka yi garkuwa da abokin ta’asarsu kan kuɗin damfara

Published

on

A ranar Litinin, 26 ga watan Disamban 2022, jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi ‘yan damfarar yanar gizo ne, waɗanda ake yiwa laƙabi da ‘yan yahoo, bisa laifin yin garkuwa da abokin aikinsu akan raba kuɗaɗen da suka samu harkarsu ta damfara da zamba cikin aminci.

Mai magana da yawu rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, SP Abimbola Oyeyemi ya shaida wa Neptune Prime Hausa cewa waɗanda ake zargin, Agbe Simeon da kuma wata mace mai suna Messiah Nicky sai Oladapo Dolapo da kuma Yetunde Shonola wacce ita ma mace ce, an kama su ne a ƙauyen Orile imo da ke ƙaramar hukumar Obafemi Owode a jihar Ogun, biyo bayan wani bayani da ‘yan sanda suka samu a garin.

KU KUMA KARANTA:Dubun wata mace da ta ƙware a garkuwa yara ta cika

‘Yan sandan da ke aiki a sashin Owode Egba, sun shaida cewa wani mutum mai suna Haruna Usman, wanda aka yi garkuwa da shi tun ranar Alhamis, 22 ga watan Disamban 2022, an yi garkuwa da shi a wani wuri a Orile Imo, bayan bayyanar labarin ne sai DPO na yankin Owode Egba, CSP Popoola Olasunkanmi, yayi gaggawar tattara mutanensa tare da kutsawa yankin, inda aka cafke huɗu daga cikin wadanda suka yi garkuwa da Haruna Usman, yayin da wasu biyu suka tsere.

Kuma binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wanda aka yi garkuwa da shi da waɗanda ake zargin ‘yan ƙungiyar damfara ne ta yanar gizo, kuma a kwanan baya sun damfari wani wanda har yanzu ba a san sunan sa ba akan kuɗi naira miliyan ashirin da shida da ɗari huɗu da talatin da bakwai da ɗari tara da hamsin (N26,437,950). ), amma wanda abin ya shafa ya ba sauran abokan aikin sa Naira miliyan biyu da dubu ɗari biyu kawai, (N2,200,000) inda ya shaida masu cewa, ba a biya kuɗin gaba ɗaya ba.

Hakan ne ya fusata abokan harkallar tada inda daga nan suka kai shi wani gida da ke Orile Imo suka yi garkuwa da shi a can tun ranar Alhamis, 22 ga Disamba, 2022, tare da barazanar kashe shi a can idan ya ƙi ba su cikakken kasonsu.

Amma a lokacin da suke wajen, bayanai sun isa ga ‘yan sandan da suka shiga, inda suka ceto wanda aka yi garkuwa da shi, suka kuma cafke huɗu daga cikin waɗanda suka shirya garkuwar, yayin da wasu suka tsere.

A halin da ake ciki, kwamishinan ‘yan sandan jihar Ogun, CP Lanre Bankole, ya bayar da umarnin a miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin yaƙi da satar mutane na sashen binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Masu yaudarar ‘yan mata ta Facebook suna yi masu fyade, tare da garkuwa da su sun shiga hannu | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Yadda ‘yan sanda suka kuɓutar da Ba’amurkiyar da ɗan Yahoo ya yaudara | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like