Connect with us

'Yansanda

Yadda ‘yan sanda suka ceto ɗan jarida daga hannun masu garkuwa da mutane

Published

on

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun a ranar 11 ga Maris, 2023, sun ceto wani ɗan jarida mai suna Oduneye Olusegun, wanda wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a unguwar Mobalufon da ke Ijebu Ode a ranar 9 ga watan Maris, 2023.

A wata sanarwa da Abimbola Oyeyemi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, ya sanyawa hannu, ya ce an yi garkuwa da ɗan jaridar wanda ya fito domin zuwa Abeokuta a unguwar Mobalufon a cikin motarsa ƙirar ​​Toyota Camry da misalin karfe 7:50 na yammacin ranar Alhamis 9 ga watan Maris, 2023.

Washegari da safe masu garkuwan suka ƙira matarsa ​​ta wayarsa inda suka buƙaci a basu naira miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan sanda suka ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Zamfara

“Bayan da kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Frank Mba ya sami labarin, sai ya umurci babban DPO na yansandan da ke aiki a unguwar Obalende ta jihar, SP Murphy Salami, wanda hurumin sa ne inda lamarin ya faru domin tabbatar da ceto ɗan jaridar.

“A bisa bin umarnin Kwamishinan, DPO ya tattara jami’ansa tare da gudanar da bincike bisa fasaha da kuma bayanan sirri kan lamarin, kuma ƙoƙarinsu ya cimma ruwa lokacin da aka gano motar ɗan jaridan, ƙirar Toyota Camry a unguwar Idimu da ke Legas, inda masu garkuwar suka tafi da shi, suna jiran kuɗin fansarsa.

“Da ganin ‘yan sandan, ‘yan bindigar sun yi ta harbe-harbe inda ‘yan sandan suka mayar masu da martani, an kuma yi musayar wuta na kusan mintuna 45 kafin daga bisani suka bar motan suka ja da baya, bayan da suka samu raunuka daban-daban na harbin bindiga.

Abinbola Oyeyemi ya ƙara da cewa, ‘yan sandan sun gano motar ɗan jaridar tayi kacakaca da jinin masu garkuwa da mutane sakamakon raunukan harbin da suka samu.

“Bayan da suka fahimci cewa ‘yan sanda sun ci karfinsu, sai suka bar ɗan jarida suka yi takansu inda suka tsere da raunuka a jikinsu.”

Yace, kwamishinan ‘yan sandan, CP Frank Mba, wanda ya yabawa mutanensa kan yadda suke nuna hazaƙa wajen ceto ɗan jaridar, ya yi kira ga jama’a musamman asibitoci da masu maganin gargajiya da su sanar da ‘yan sanda idan sun ga wani da harbin bindiga ya zo neman magani wajensu.

Frank Mba ya kuma gargaɗi masu aikata laifuka da su kaurace wa jihar Ogun, saboda rundunar ta shirya tsaf domin kai farmakin a duk inda suke.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: An saki tsohon mataimakin gwamnan jihar Nasarawa da aka sace | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like