No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da ɗalibai 6 na makarantar firamare ta ƙaramar hukumar Alwaza da ke ƙaramar hukumar Doma a jihar Nasarawa su shida.

An ce ‘yan bindigar sun kai hari makarantar ne da misalin ƙarfe 7 na safiyar ranar Juma’a.

Rahman Nansel, mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar, ya tabbatar wa ‘yan jarida lamarin a ranar Juma’a.

Nansel ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike da ceto . “An tabbatar an sace ɗalibai shida.Sun mamaye makarantar da misalin karfe ƙarfe 7:10 na safe.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun nemi kuɗin fansa kan ɗaliban da suka sace a kai har Kogi

Ana ci gaba da bincike da ceto wanda Kwamishinan ‘yan sanda ya ke jagoranta yayin da ya gana tare da jajantawa iyayen waɗanda lamarin ya shafa,” in ji shi ta hanyar saƙon rubutu.

A halin yanzu dai jihar Nasarawa na ɗaya daga cikin jihohin arewa ta tsakiya da ke fama da matsalar rashin tsaro.

A tsawon shekaru ana kai hare-hare a kan al’ummar Nasarawa, wanda ya kai ga kashe-kashe, sace-sacen mutane, da kuma gudun hijira.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...