Connect with us

Al'ajabi

Yadda ruwan sama ya lalata gidaje sama da ɗari a Ekiti

Published

on

Ruwan sama da aka shafe sa’o’i biyu a ana yi a yammacin Juma’a ya lalata gine-gine 105 a Oke-Ako da ke ƙaramar hukumar Ikole ta jihar Ekiti.

Haka kuma ya lalata cibiyoyin wutar lantarki a faɗin garin, lamarin da ya jefa mutanen garin cikin duhu.

Gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, a lokacin da yake tantance lamarin da ya abku a garin, ya jajantawa mazauna yankin.

Oyebanji, wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa, Misis Monisade Afuye, ta bayyana faruwar lamarin a matsayin mummunar barna.

“Bari kuma in tabbatar muku cewa gwamnatin jihar ba za ta yi watsi da ku ba kuma ta ba ku damar yin nadama a cikin wadannan munanan yanayi.

“Za mu ba da duk wani goyon bayan da ya dace don daƙile duk wani tasiri da wannan lamarin ya haifar ga rayuwar ku,” in ji mataimakin gwamnan.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin jihar Yobe ta fara aikin tituna da magudanan ruwa

Aribasoye ya tabbatar wa jama’a cewa nan ba da daɗewa ba za a kawo ɗauki ga waɗanda abin ya shafa, inda ya buƙace su da su kasance cikin lumana kuma su samu makoma a cikin gwamnati domin su taimaka wajen dawo da asarar da suka yi.

Babban Manaja na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Ekiti, Mista Jide Borode, ya ce za a iya rage tasirin ruwan sama, idan masu gidajen sun sanya hannu kan shirin dashen itatuwa na gwamnatin jihar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Wasu jihohi a arewacin Najeriya za su fuskaci ƙarancin ruwan sama – NEMA | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like