Connect with us

Al'ajabi

Yadda magidanci ya ƙone matarsa da fetir saboda abinci

Published

on

Wani mutum mai shekara 46 mai suna Hassan Azeez ya shiga hannun jami’an ‘yan sandan jihar Ogun, bisa laifin zubawa matarsa ​​fetur da kuma cinna mata wuta.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi ya sanyawa hannu, ya ce an kama wanda ake zargin ne biyo bayan rahoton da mahaifin matar, ya shigar a sashin rundunar da ke Ibogun, wanda ya bayar da rahoton a ranar 22 ga watan Oktoban 2022, cewa mijin nata ne ya kona ɗiyarsa Olayinka Hassan saboda wani rashin jituwa a tsakanin su,ya ce an garzaya da ɗiyar tasa mai ɗa guda asibiti a da ke garin Ibadan inda ake kula da lafiyarta.

KU KUMA KARANTA:Yadda wani mutum ya kashe matar sa saboda burodi

“Bayan rahoton, DPO reshen Ibogun, CSP Samuel Oladele ya yi gaggawar tattara mutanensa suka nufi wurin, amma kafin su isa wurin, wanda ake zargin ya tsere.

“Tun daga lokacin ne jami’an ‘yan sanda ke bin sahunsa har zuwa ranar 22 ga watan Janairu inda a ƙarshe aka kama shi.

“Da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya yi ikirarin ya gudu zuwa jamhuriyar Benin ya kuma amsa laifinsa, amma ya ɗora laifin a kan shaiɗan.

Hassan Azeez, wanda ake zargi

“A cewarsa, ya bukaci matar tasa ta shirya masa abinci, amma maimakon ta shirya masa abincin, sai ta shagaltu da yin wanki.

“Ya ci gaba da cewa ya fusata ne saboda yunwar da yake ji, abun da ya sa shi zuba mata man fetur ya banka mata wuta.

“Lokacin da aka tambaye shi kayan wa matar ke wankewa a lokacin, sai ya amsa da cewa kayan sa ne” Oyeyemi ya ce .

A halin da ake ciki, kwamishinan ‘yan sanda, CP Lanre Bankole, ya bayar da umarnin a mika wanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na ‘yan sanda a jihar domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da shi gaban kuliya.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Tayi ƙunar bakin wake ta kashe kanta saboda bashin naira dubu saba’in | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like