Connect with us

Ƙasashen Waje

Yadda likitoci suka koma yin tiyata a barandar asibitoci saboda rashin ɗakuna a Gaza

Published

on

Asibitoci sun yi gargaɗin cewa mutane da dama za su rasu saboda rashin kayan aiki.

A lokacin da Asibitin Indonesia na Gaza yake samu ƙaruwar majinyata da suka samu munanan raunuka a dalilin hare-haren bama-baman Isra’ila, likitoci sun koma shirya wani ɗan wajen yin tiyata a barandar asibitin saboda asalin ɗakunan tiyatar sun cika, in ji su.

Saboda yadda ƙarancin magunguna da rashin wutar lantarki da hare-haren bama-bamai suke shafar asibitoci, dole likitoci a Gaza suka koma aiki ba dare ba rana domin kula da majinyatan da ake kawo musu kusan a kowane lokaci.

“Muna yin awa ɗaya-ɗaya ne saboda ana iya kawo mana waɗanda suka samu rauni a kowane lokaci.

“A lokuta da dama mukan yi tiyata a baranda, ko kuma a ɗakunan zaman masu kula da majinyata,” in ji Dakta Mohammed al Run.

Ya yi wannan jawabin ne jim kaɗan bayan harin bam ya bugi wani sashe a Asibitin Indonesia, wanda yake kusa da hanyar da sojojin Isra’ila ke ƙara ƙaimin kutsawa domin shiga yankin na Falasɗinu mai ɗimbim mutane, da kuma yadda suke ganin alamar man fetur ɗinsu ya kusa ƙarewa kamar yadda likitocin suka bayyana.

KU KUMA KARANTA: An kashe ma’aikatan Majalisar Ɗinkin Duniya 64 a Gaza

Tankokin Isra’ila sun shiga Gaza, mazaunin mutum miliyan 2.3 bayan kimanin mako uku suna jefa bama-bamai a yankin saboda mayar da martani a kan harin mayaƙan Hamas na ranar 7 ga Oktoba inda suka yi awon gaba da mutum 240 ’yan Isra’ila.

Ma’aikatan lafiya a yankin wanda ke ƙarƙashin Hamas sun ce an kashe sama da mutum 8,500 a hare-haren na Isra’ila a Gaza, ciki har da ƙananan yara 3,500.

A Arewacin Gaza, inda Isra’ila ta umarci miliyoyin mutane su bar gidajensu su koma kudancin yankin, samun kiwon lafiya na cikin abubuwa da suka fi wahalar gaske.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like