No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wata mata mai shekaru 53 da haihuwa, wadda ake zargin an same ta da tarin kayan zaɓe da aka rufe.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Legas SP Benjamin Hundeyin, ne ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN), a ranar Juma’a.

KU KUMA KARANTA: Hukumar DSS ta ƙwato makamai a jihohi daban-daban biyo bayan hare-haren siyasa a Kano

Hundeyin ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Alhamis da misalin karfe 4:00 na yamma, a kan titin Candos, da ke Baruwa a unguwar Iyana-Ipaja a Legas, ya ƙara da cewa an kama wadda ake zargin ne a cikin wata cibiyar kasuwanci inda take buga takardun.

Ya ce, “An kama ta ne da kayan INEC 550 daban-daban. Laptop ɗin da ta yi amfani da shi wajen buga kayan an dawo da ita kuma ta kasa yin cikakken bayani kan yadda ta mallaki kayan.

“An mayar da shari’ar zuwa CID Yaba a Legas don ci gaba da bincike.” In ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...