No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani mutum mai suna Iduh Hausa ya harbe sirikinsa har lahira, wato mijin ƙanwarsa, bisa zarginsa da cin amana tare da bibiyar matan banza, lamarin da ya abku a garin Umunede da ke ƙaramar hukumar Ika ta Arewa maso Gabas a jihar Delta.

Lamarin wanda ya jefa al’ummar yankin cikin alhini, wata majiya ta ce ana tada jijiyoyin wuya a tsakanin al’umma dangane da abkuwwar lamarin.

“Mista Iduh Hausa ya harbe surukin nasa har lahira saboda kawai yana zarginsa da yin soyayya da wata mace, ya ce surukin nasa yana yaudarar ‘yar uwar sa.”

KU KUMA KARANTA:A gabana ‘yan sanda suka kashe makiyaya, bayan Abba Kyari ya nemi in ɗorawa Saraki laifin fashi – Ɗan fashi ga Kotu

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Bright Edafe, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “Eh, ya tabbata; ba mu kama wanda ake zargi ba; har yanzu yana nan. Ana ci gaba da kokarin kama shi a duk inda ya ke ɓoye.” inji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...