No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Burundi, Evariste Ndayishimiye, ya bayar da shawarar cewa ya kamata a fara jefe masu aikata laifin auren jinsi a gaban taron jama’a

Evariste Ndayishimiye, ya kuma caccaki ƙasashen Yammacin duniya, kan yadda suke matsawa ƙasashen da ke kyamar auren jinsi lamba.

Tun a shekarar 2009 aka kafa dokar yanke zaman shekaru biyu a gidan yari ga duk wanda aka samu da laifin aikata luwaɗi ko kuma auren jinsi a Burundi, ƙasar da ta kasance mai tsatssauran ra’ayin addinin kirista a gabashin Afirka.

Ndayishimiye, wanda ya kasance mabiyin ɗarikar Katolika, ya ce auren jinsi haramun ne a addinin kiristancci kuma abin kyama ga al’adun ƙasar.

“Ni dai a ganina, idan muka samu irin waɗannan mutane da aikata auren jinsi ko kuma luwaɗi, to kuwa babu abin da ya kamace su, shine a samu babban filin taro a ajiye su, tare da ƙiran taron jama’a domin jefe su,” in ji Ndayishimiye.

KU KUMA KARANTA: An kama matashi kan zargin luwaɗi da ɗan shekara 4 a Gombe

Ya kuma yi tir da yadda ƙasashen Yamma ke matsawa ƙananan ƙasashe ala tilas sai sun halasta auren jinsi ko kuma a ddaina basu taimakon jin kai.

Ya ce, ‘yan Burundi da ke rayuwa a ƙasashen waje, waɗanda suka rungumi akidar auren jinsi su ci gaba da zama a can, ba sai sun koma ƙasar ba.

Auren jinsi dai haramun ne a ƙasashen gabashin Afirka dda dama, waɗanda ke da tarihin nuna kyama ga masu aikata hakan, da kuma nuna musu kyama, musamman waɗanda suka rungumi koyarwar addinin musulunci ko kuma kiristanci.

A watan Mayu ne, ƙasar Uganda, ta ayyana hukunci mai tsauri ga duk wanda aka samu da aikata auren jinsi, abin da ya fuskanci suka daga ƙasashen yammaci da ƙungiyoyinsu.

Hakan ta sanya a wancan lokaci, Amurka ta ce za ta cire ƙasar Uganda daga cikin ƙasashen da take hulɗar kasuwanci da ssu, tare da haramta bayar da bisa shiga ƙasar ga manyan jami’anta, inda bankin bayar da lamuni na duniya, IMF ya dakatar da sabon Shirin bayar da bashi ga ƙasar.

A watan Maris ɗin wannan shekarar ne, Burundi ta yanke wa mutum 24 hukuncin zaman gidan yari, bayan samunsu da laifin auren jinsi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...