Connect with us

Labarai

Ya kamata a duba batun ‘mafi ƙarancin albashi’, Tinubu ya gayawa gwamnonin APC

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa mafi ƙarancin albashi na ƙasa na buƙatar bita don nuna haƙiƙanin gaskiya, yana mai jaddada cewa inganta rayuwar ‘yan Najeriya shi ne babban abin da gwamnatinsa ta sa a gaba.

Shugaban wanda ya karɓi baƙuncin membobin ƙungiyar gwamnonin Progressive Forum (PGF) ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Hope Uzodinma na jihar Imo a fadar gwamnati, ya ce gwamnatocin ƙasa da na ƙananan hukumomi za su yi aiki kan mafi ƙarancin albashi, wanda tuni ya buƙaci “neman rai”

A cewar sanarwar da daraktan yaɗa labarai na fadar gwamnatin jihar, Mista Abiodun Oladunjoye, Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ƙara yin aiki kan wasu manufofin tattalin arziƙi da suka shafi jama’a.

“Muna buƙatar yin wasu ƙididdiga da binciken mai amfani akan mafi ƙarancin albashi. Dole ne mu kalli wannan tare, da kuɗaɗen shiga.

KU KUMA KARANTA: Za mu yi amfani da tsofi da sababbin takardun kuɗi a Najeriya – Tinubu

Dole ne mu ƙarfafa tushe da kuma amfani da kuɗaɗen shigarmu,” inji shi. Tinubu ya buƙaci Gwamnonin da su yi amfani da damar da aka basu na zaɓar su a cikin miliyoyin ‘yan ƙasa a Jihohinsu domin kawo sauyi a rayuwar al’umma, inda ya ƙara da cewa zai yi aiki don amfanin ‘yan Najeriya.

“Wannan taron ba baƙon abu bane a gare ni, kuma abubuwan da taron ya ƙunsa yana da matuƙar amfani.

Abokan hulɗa yana da ban sha’awa sosai. Wannan ya shafi aikin Najeriya ne ba Bola Tinubu ba,’’ inji shi.

Shugaban ya ce za a daidaita yawan kuɗaɗen musaya, yana mai cewa tsarin mulki na ci gaba.

“Na gaji kadarori da kuma bashin wanda ya gabace ni. Wannan shi ne karon farko da kuka shiga zauren majalisar, kuma wannan ne karo na farko da zan yi taro.

“A matsayinku na masu ci gaba kuma masu tunani a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), kuna da rawar da za ku taka wajen wayar da kan jama’armu da kuma tabbatar da cewa mun gudanar da kanmu,” in ji Shugaban ya shaida wa Gwamnonin.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Remi Tinubu ta fara aiki a matsayin matar shugaban ƙasa | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamnatin Edo ta ƙara albashi mafi ƙaranci zuwa dubu 40,000, ta rage ranakun aiki zuwa sau uku a mako | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Ba a ƙara wa shugaban ƙasa, mataimakinsa, zaɓaɓɓun ‘yan majalisa da alƙalai albashi ba – Gwamnatin tarayya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like