Connect with us

Al'ajabi

Ya je karɓo ‘ya’yansa a wajen tsohuwar matarsa, ‘yan’uwanta sun kashe shi da duka

Published

on

Wani ɗan kasuwa mai suna Mallam Umar Tasiu, ya sha bulala, wadda ta yi sanadiyyar mutuwarsa har lahira da wasu surukansa suka yi masa a garin Minna na jihar Neja.

Wani maƙwabcinsa ya shaida wa Daily trust cewa, marigayin wanda ya kammala karatunsa a Jami’ar Al Azhar da ke Masar ya je ganin ‘ya’yansa da ke zaune da tsohuwar matarsa a gidan mahaifinta.

“Ya je ya ga ‘ya’yansa guda biyu da suke zaune tare da tsohuwar matarsa a gidan mahaifinta.  Sun rabu amma yaran suna wurin mahaifiyarsu. Ya je ya gansu amma surukansa na baya ba su so ya zo gidansu. 

Bayan isarsa sun ɗaure shi suka yi masa bulala har ya mutu a gidansu. An dawo da gawarsa gidansa a daren ranar Asabar kuma mun binne shi a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na safe,” inji majiyar.

KU KUMA KARANTA: An kama waɗanda ake zargi da kashe wata mata, ta hanyar yi mata yankan rago a Gwambe

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, DSP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mamacin ya rasu ne bayan an kai shi Asibitin ƙwararru na IBB da ke Minna, sakamakon raunukan da wasu ‘yan daba suka yi masa da bulala a gidan surukansa.

“A ranar 22/10/2023 da misalin ƙarfe 08:00, an samu rahoton ƙorafi kan aikata laifin kisan kai a sashin GRA;  cewa a ranar 21/10/2023 da misalin ƙarfe 23:00 wasu ‘yan daba suka kai wa wani Umar Tasiu ɗan Angwan Daji hari a Minna kuma ya samu munanan raunuka. 

An garzaya da shi Asibitin IBB da ke Minna, inda ya rasu. Ana ci gaba da bincike kan lamarin kuma ana ci gaba da ƙoƙarin kama waɗanda ake zargin,” in ji PPRO.

Wani abokin marigayin, Ahmad Sallah, a wani saƙon da ya wallafa a Facebook ya ce tsoffin surukai sun ƙi amincewa da auren ɗiyarsu da Umar saboda bambancin aƙidar addini.

“An yi wa Malam Umar duka har lahira a gidan surukinsa.  Alaramma mallam Umar tasi’u ɗan marigayi Alh Tasiu mai yadi.  Alaramma ɗan kasuwa ne, Hafiz, muhaddith, ya yi aure bayan ya kammala digirinsa a Jami’ar Al Azhar Egypt,” ya rubuta.

“Da alama ya fuskanci wani mawuyacin hali da tsohon surikinsa, wanda a ƙarshe ya yi sanadiyyar mutuwarsa, Alaramma Mallam Umar mutum ne mai kishin ƙasa, ɗan kasuwa ne, Hafiz, kuma muhadisi, ya kammala digirinsa a Jami’ar Al Azhar da ke Masar kafin ya yi aure.

“Ya bayyana cewa dangin matarsa suna da bambancin akidar addini, mahaifinta ɗan Izala ne, shi kuma ɗan ɗarikah ne, duk da rashin amincewar mahaifinta, sun yi aure sun haifi ‘ya’ya uku tare.

“Abin takaicin shi ne, saboda matsalar kuɗi a kasuwancin Alaramma, mahaifin matarsa ya yanke shawarar raba su, ya kai ƙarar Alaramma a gaban kotu, yana zargin Alaramma da koyar da ‘yarsa aƙidar ɗariqah.

“Duk da haka, Alaramma ya samu nasarar kare kansa a gaban kotu ta hanyar amfani da iliminsa mai yawa, duk da cewa ya ci nasara, mahaifin matarsa ya ɗauke ta da ƙarfin tsiya daga wurinsa, watau gidan Alaramma, lamarin da ya sa ala dole suka rabu aure ya mutu.

“Bayan shekaru, mahaifin har yanzu ya kwashe yaran daga hannun Alaramma.  Abin takaici, a lokacin da ya je gidan surukinsa yake yunƙurin karɓo ’ya’yansa daga hannun tsohuwar Matarsa da surukinsa, sai suka ƙira shi ɓarawo, yanayi da ya sa aka kai masa hari da duka ya mutu har lahira.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like