Connect with us

Laifi

Ya binne ƙaninsa da rai, bayan ya yi masa duka, kan zarginsa da sata

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta kama wani matashi mai suna Goodness Oshodi mai shekaru 19 da haihuwa da ake zargin ya binne ƙaninsa mai suna Friday Oshhodi da ransa bisa zargin satar Naira 1000.

Lamarin ya faru ne da yammacin talata 10 ga watan Oktoba, 2023, a unguwar Apamisede, a ƙaramar hukumar Adavi ta jihar.

Sai dai wanda abin ya shafa ya yi sa’a da maƙwabta sun ceto shi.

A cewar shaidun gani da ido, mahaifiyar Goodness ta umarce shi da ya hukunta Friday bisa zargin satar mata Naira 1,000.

 An tattaro cewa Goodness ya lakaɗa wa Friday duka kafin ya binne shi da rai.

KU KUMA KARANTA: Ɗan fari ya kashe ɗan autansu da duka, ya raba kansa gida biyu

Da yake magana kan dalilin da yasa ya yanke shawarar binne ɗan uwansa da rai, Goodness ya ce yana aiwatar da umarnin mahaifiyarsu ne kawai da ta buƙaci ya hukunta ɗan uwansa bisa zargin satar mata Naira 1000 da ƙoƙarin gudu.

A cewarsa, mahaifiyar wadda ta umarce shi da ya hukunta Friday, ta je coci lokacin da ya binne shi da rai.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP William Aya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kama yaron kuma ana yi masa tambayoyi.

“Eh, muna sane.  An kama yaron, ana ci gaba da gudanar da bincike kan dalilin da ya sa kuma ta yaya hakan zai iya faruwa,” PPRO ya ƙara da cewa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

Published

on

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

An kama ɗan sandan da ya yi wa matashiya fyaɗe a Legas

An kama ASP Owolabi, jami’in ɗan sandan da ake zargin ya yi wa wata matashiya mai shekara 17 a duniya fyaɗe a ofishin ’yan sanda na Ojota da ke Jihar Legas.

Ana zargin lamarin ya faru ne a ofishin Owolabi, lamarin da ya sa hukumar kula da cin zarafin mata ta Jihar Legas ta ɗauki matakin gaggawa.

Wasiƙar da aka aike wa Kwamishinan ’yan sandan jihar, Adegoke Fayoade, ya kai ga kama jami’in tare da fara bincike cikin gaggawa.

Kakakin rundunar jihar, Benjamin Hundein, ya tabbatar da kama jami’in, ya kuma tabbatar wa jama’a cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

Kwamishinan ya jadadda aniyar cewar idan aka samu jami’in da laifi zai fuskanci hukunci mai tsauri bisa dokokin ’yan sanda da doka.

KU KUMA KARANTA: Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Ya sake jaddada wa jama’a jajircewar rundunar na kiyaye dokoki da kuma kare jama’a.

Mahaifiyar yarinyar, Misis Aramide Olupona, ta zargi ‘yan sanda da yunkurin yin rufa-rufa kan lamarin, wanda hakan yake barazana ga lafiyar ’yarta.

Duk da yunƙurin da iyalan jami’in da kwamandan yankin suka yi na warware lamarin cikin masalaha, mahaifiyar yarinyar ta ce sai inda ƙarfinta ya ƙare don ganin an yi wa ’yarta adalci.

Lamarin ya faru ne bayan da ɗan sandan ya yi ƙoƙarin taimakon yarinyar wajen gano wayarta da aka sace.

Daga bisani ya yaudare ta zuwa ofishinsa wanda a nan ne ake zargin ya yi mata fyaɗe.

Continue Reading

Laifi

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Published

on

'Yan bindiga sun sace 'yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

‘Yan bindiga sun sace ‘yan jarida 2 da iyalansu a Kaduna

Daga Idris Umar, Zariya

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ‘yan jarida biyu a ƙauyen Danhonu da ke ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kai hari a cikin al’umma a daren ranar Asabar inda suka yi awon gaba da ‘yan jarida biyu da iyalansu.

Waɗanda abin ya shafa, Alhaji AbdulGafar Alabelewe da AbdulRaheem Aodu, ‘yan jarida ne na jaridun The Nation da Blueprint a jihar Kaduna, bi da bi.

Alabelewe wanda shi ne shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), majalisar jihar Kaduna a halin yanzu, an dauke shi tare da matarsa da ‘ya’yansa biyu.

An kuma yi garkuwa da Aodu da matarsa, inda suka bar ‘yarsu da ba ta da lafiya.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

Da yake bayyana hakan, Taofeeq Olayemi, dan uwa na daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya ce ‘yan bindigar sun afkawa al’ummar ne da misalin karfe 10:30 na dare, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su yi awon gaba da su.

Da farko ‘yan fashin sun tafi da Alabelewe, matarsa, ‘ya’yansa uku, da kuma wani bako, amma daga baya suka sako yarinyar daya daga cikin yaran.

“Sun shiga gidan Abdulgafar ta katanga.

“Sun shiga cikin ɗakin kwanansa kai tsaye suka ɗauko shi da matarsa da ‘ya’yansu biyu suka tafi nan take, inda ‘yan banga suka iso suka fara harbin iska,”

Ya zuwa haɗa wannan rahoton babu ɗuriyar duk wanɗana aka sacen.

Tuni kunyar ‘yan jaridar ta jihar Kaduna ta sanar tare da tabbatar da faruwar lamarin.

Continue Reading

Laifi

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Published

on

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Ana zargin wani matashi mai suna Ufuoama Umurie ya kashe mahaifinsa a Unguwar Okpare da ke Ƙaramar Hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, ranar Laraba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, an tsinci gawar mahaifin mai suna Rabaran Isaac Umurie, wanda ɗaya ne daga cikin limaman cocin St. John’s Anglican da ke Okpare-Olomu a safiyar wannan Larabar.

Bayanai sun ce tun farko lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar dare, inda wanda ake zargin ya kori mahaifiyarsa a lokacin da take ƙoƙarin ceto rayuwar mijinta amma ita kanta da ƙyar ta tsira.

Ufuoma, wanda a halin yanzu yana hannun ‘yan sanda, an ce ya yi amfani da laujen yankar ciyawa ya yanka mahaifinsa sannan ya sassare shi a sassan jikinsa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni sun ce matashin ya yi wa mahaifinsa wannan aika-aikar ce a lokacin da yake barci kafin maƙwabta da mabiya cocin su su kawo ɗauki.

Duk da cewa har yanzu ba a gano abin da ya haddasa faruwar lamarin ba, wasu mazauna unguwar yankin sun yi zargin cewa Ufuoma yana fama da taɓin hankali, kuma wannan ne karo na biyu da ya kai wa mahaifin nasa hari.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like